Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin
Labaran Cikin Gida

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Nig Police force

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta tabbatar da aukuwar wani mummunan lamari a ranar 25 ga Mayu, 2025, da misalin karfe 8:15 na dare a karamar hukumar Rano, inda aka kama wani mai gyaran babur mai suna Abdullahi Musa, ɗan asalin Rano, bisa zargin tuƙin babur cikin haɗari da kuma yiwuwar kasancewa cikin maye, bayan korafe-korafe daga jama’a.

Bayan an tsare shi, sai ya fara nuna alamun rauni, wanda ya sa aka garzaya da shi Asibitin Gwamnati na Rano, inda ya rasu a safiyar ranar 26 ga Mayu, 2025, da misalin karfe 6:00 na safe yayin da ake kula da lafiyarsa.

Biyo bayan rasuwar tasa, wasu fusatattun matasa suka kai farmaki ofishin ‘yan sanda na Rano, tare da kone wani sashi na ofishin da motoci guda biyu, suka lalata wasu motoci goma (10), sannan suka jikkata DPO mai kula da ofishin. An garzaya da DPO ɗin zuwa Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, inda daga bisani ya rasu yana karɓar kulawa.

Rundunar Yan sandan ta Kuma ce ta kama mutane ashirin da bakwai (27) da ake zargi da hannu a wannan ta’asa. An kwantar da tarzomar, kuma an dawo da zaman lafiya da doka a yankin.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, PhD, ya kai ziyara wurin da lamarin ya faru, sannan ya kai gaisuwar ta’aziyya ga Mai Martaba Sarkin Rano, Ambasada Dakta Mohammed Isah Umar (Autan Bawo 19). Ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin lamarin da daukar matakin doka kan duk wanda aka samu da laifi.

Hukumar ‘yan sanda ta Jihar Kano na jajantawa iyalan marigayi DPO, wanda ya rasa rayuwarsa a bakin aiki, tare da roƙon jama’a da su kwantar da hankalinsu, su guji ɗaukar doka a hannunsu, su kuma bai wa hukuma hadin kai wajen gudanar da bincike cikin kwanciyar hankali.

Hukumar na tabbatar da kudirinta na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da doka a jihar, tare da neman goyon bayan al’umma a wannan lokaci.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025

NAPTIP ta kama mutane biyar da ake zargi da safarar mutane

October 2, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.