Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » NAPTIP ta kama mutane biyar da ake zargi da safarar mutane
Afrika

NAPTIP ta kama mutane biyar da ake zargi da safarar mutane

October 2, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
naptip

Hukumar Yaƙi da Safarar Mutane ta Najeriya (NAPTIP) ta bayyana cewa ta cafke mutum biyar da ake zargi da hannu a safarar mutane tare da kuɓutar da mutum 24 a filin jirgin sama na kasa da kasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Vincent Adekoye, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, inda ya ce cikin waɗanda aka kama har da wani mutum da ya yi ƙoƙarin safarar ‘yarsa zuwa ƙasar Iraƙi.

Jami’in Ɗan Sanda Ya Harbe Kansa Da Bindiga Bisa Kuskure A Kano

Wannan samame ya biyo bayan bayanan sirri ne da hukumar ta samu, kuma an gudanar da shi ƙarƙashin jagorancin Babbar Daraktar NAPTIP, Binta Adamu Bello.

Adekoye ya ce cikin waɗanda aka kama akwai wani babban jami’in tsaro da ake zargi da kasancewa cikin ƙungiyar masu safarar mutane a yankin kudu maso yamma na ƙasar.

> “Mun kuɓutar da yara da matasa masu shekaru tsakanin 15 da 26, waɗanda aka ɗauko daga jihohin Kano, Katsina, Oyo, Ondo da Ribas, kuma suna kan hanyarsu ta zuwa ƙasashen Iraƙi, Sudan, Masar, Saudiyya, Bahrain da Afghanistan,” in ji shi.

Adekoye ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka kuɓutar ta bayyana cewa za ta tabbatar da an gurfanar da mahaifinta a kotu kan yunƙurin safararta da ya yi zuwa Iraƙi.

Haka kuma, wata daga cikin waɗanda aka yi ƙoƙarin safarar ta ce mahaifiyarta ce ta tilasta mata ta amince da tafiya zuwa Turai domin yin aiki da za ta rika samun daloli.

Hukumar NAPTIP ta jaddada cewa za ta ci gaba da kai sama-samar da ayyuka na musamman tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro domin ƙarfafa yaƙi da safarar mutane da kuma tabbatar da cewa duk wanda aka kama da hannu a irin wannan laifi ya fuskanci hukunci.

abuja Featured naptip
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026

An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje

April 24, 2026

El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi

April 21, 2026

Dole Najeriya ta samu tsaro – Babban hafsan tsaro

April 20, 2026

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.