Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano
Afrika

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
AB
AB

Gwamnatin jihar Kano dake arewacin Najeriya ta yi watsi da rahotannin da ake yaɗawa cewa akwai rashin jituwa tsakanin Gwamnan Jihar Abba Kabir Yusuf da kuma jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

A ranar Litinin ne jaridar Daily Nigerian ta fitar da wani labari wanda ke zargin cewa gwamnan Kano Abba Kabir ya daina ɗaukar kiran wayar uban gidansa Sanata Rabiu Kwankwaso, lamarin da hakan ya tayar da ƙura a kafofin sada zumunta.

Sai dai a wata sanarwa da babban mai taimakawa gwamnan Kano kan kafofin sada zumunta Salisu Yahaya Hotoro ya fitar, ya ce babu wata rashin jituwa tsakanin Gwamna Abba da mai gidan nasa Kwankwaso.

“Gwamna Abba K Yusuf ya himmatu sosai wajen tabbatar da akidu da hangen nesa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP). Ya himmatu wajen samar da hadin kai a cikin jam’iyyar tare da yin aiki tare da dukkan ‘ya’yan jam’iyyar ciki har da Kwankwaso domin cim ma burinmu,” kamar yadda sanarwar ta ƙara da cewa.

“Wannan zargin ba gaskiya bane kuma karkatar da hankali ne sakamakon Abba yana da ladabi da alaƙa mai kyau da Rabiu Kwankwaso, inda yake kallonsa a matsayin jagora a jam’iyya da kuma tafiyarsa ta siyasa. Duk wata magana ta ɓaraka a tsakaninsu batu ne kawai na zuzutawa, amma ya saɓa wa mu’amularsu ta aiki,” in ji sanarwar.

A ‘yan kwanakin nan ana ta samun raɗe-raɗin rashin jituwa a tsakanin gwamnan na Kano da kuma Kwankwaso inda har wasu da ba a tabbatar da ko su wane ne ba suka fitar da wata tafiya mai suna Abba Tsaya da Kafarka, wadda ke nufin Abban ya ƙaurace wa Kwankwaso.

A ranar Litinin ne Dan majalisar wakilan jihar daga karamar hukumar Dala Aliyu Sani Madakin Gini da takwaransa na kananan hukumomin Rano da Bunkure da kuma Kibiya a majalisar wakilan kasar suka sanar da barranta kansu da tafiyar Kwankwasiyya a jihar.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.