Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » “Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”
Labaran Cikin Gida

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260711 WA0013

Rikicin da ya shafi bayar da shaidar zama ɗan ƙasa a Ƙaramar Hukumar Jos North ta Jihar Filato ya ɗauki sabon salo, bayan da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jos North, ƙarƙashin jagorancin Ujah Anaguta, Mai Martaba Pozoh Johnson, tare da Ƙungiyar Cigaban Anaguta (Anaguta Development Association) da wasu ƙungiyoyi suka nemi Babbar Kotun Jihar Filato ta ba su damar shiga cikin shari’ar da ke tsakanin Fatima Baba Akawu da Ƙaramar Hukumar Jos North.

A zaman kotun da aka gudanar ranar Juma’a, lauyoyin ɓangarorin biyu sun yi muhawara kan buƙatar masu neman shiga cikin shari’ar. Lauyoyin nasu sun ƙalubalanci halascin bayyanar wasu manyan lauyoyi masu mukamin SAN da ke wakiltar mai ƙara, suna masu cewa ba su kasance cikin shari’ar tun daga farkonta ba, kuma babu wata takardar da ta nuna an sauya lauyan da ya fara gudanar da karar.

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

Sai dai lauyoyin ɓangaren mai ƙara da na Ƙaramar Hukumar Jos North sun yi fatali da waɗannan hujjoji, inda suka gabatar wa kotu da dalilai da tanade-tanaden doka da suka ce sun tabbatar da sahihancin matsayinsu.

Bayan sauraron hujjojin kowane ɓangare, Alƙalin Babbar Kotun Jihar Filato, Mai Shari’a Justice C. Donglong, ya ɗage yanke hukunci kan buƙatar shiga cikin shari’ar zuwa ranar 29 ga Oktoban 2026.

A cikin ƙudurin da Ƙaramar Hukumar Jos North ta gabatar a gaban kotu, ta nemi a soke hukuncin da aka yanke ranar 9 ga Yunin 2026, tana mai cewa ba a bi ƙa’idojin shari’a da suka dace ba. Karamar hukumar ta yi zargin cewa ba ta samu sahihin sammaci ko takardun sauraron ƙara ba, lamarin da ta ce ya tauye mata haƙƙinta na samun cikakken sauraro kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada.

Har ila yau, ta bayyana cewa takardar sanarwar sauraron ƙara da aka taɓa aikewa gare ta ta fito ne daga Babbar Kotun Pankshin, alhali shari’ar tana gudana a Babbar Kotu ta 17 da ke West of Mines, inda ta ce an ci gaba da shari’ar ba tare da saninta ko wakilcinta ba.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

NWUK Expels 34 Students Over Examination Malpractice

June 30, 2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 2026

NDLEA Ta Kone Tan 12.2 Na Miyagun Ƙwayoyi a Kano, Ta Kama Mutum 

June 29, 2026

YAƘI DA SHA DA FATAUCIN MIYAGUN ƘWAYOYI A KANO: Babban Kalubale Ne Ke Gaban Kwamitin Muhuyi Rimingado

June 26, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.