Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari
Babban Labari

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Permanent Voters Cards PVCs from Officials of the Independent National Electoral Commission INEC 2 (1)

Mai Martaba Sarkin Gaya, Dakta Ali Ibrahim Abdulkadir, ya yi kira ga al’ummar Masarautar Gaya da su rungumi rajistar katin zaɓe tare da tabbatar da mallakarsa, yana mai jaddada cewa katin zaɓe shi ne ginshiƙin dimokuraɗiyya kuma hanya mafi inganci ta zaɓen shugabanni nagari.

Sarkin ya bayyana hakan ne lokacin da ya karɓi baƙuncin Shugaban Ƙaramin Kwamitin Kartakwana kan Rajistar Katin Zaɓe (CVR) na Ɗan Malikin Kano, Kwamared Auwalu Mudi Yakasai, wanda ya jagoranci tawagar kwamitin zuwa masarautar domin wayar da kan jama’a kan muhimmancin katin zaɓe.

Tun da farko, Kwamared Auwalu Mudi Yakasai ya ce kwamitin ya samu gagarumin goyon baya daga masarautun gargajiya a faɗin jihar, yana mai bayyana cewa sarakuna na taka muhimmiyar rawa wajen isar da saƙonnin ci gaba ga al’umma.

Ya ce kwamitin ya lura cewa haɗin kan da ake samu daga sarakuna ya ƙara ƙarfafa gangamin wayar da kai kan rajistar katin zaɓe, domin katin zaɓe shi ne haƙƙin kowane ɗan ƙasa kuma makamin tabbatar da shugabanci nagari.

A cewarsa, mallakar katin zaɓe na bai wa ɗan ƙasa damar zaɓar shugabannin da yake da yaƙinin za su kare muradunsa tare da kawo ci gaba, yana mai ƙara da cewa dimokuraɗiyya ba za ta bunƙasa ba idan jama’a ba su fito sun yi rajista tare da amfani da katunansu wajen zaɓe ba.

Da yake nasa jawabin, Sarkin Gaya ya ce ya zama wajibi kowane ɗan ƙasa da ya cancanta ya mallaki katin zaɓe, domin ita ce hanya mafi dacewa ta tabbatar da shugabanci nagari, adalci da ci gaban al’umma.

Sarkin ya kuma umarci dukkan hakimai da masu unguwanni da ke ƙarƙashin Masarautar Gaya da su ƙara himma wajen wayar da kan jama’a kan muhimmancin rajistar katin zaɓe da kuma fitowa domin kaɗa ƙuri’arsu a lokacin zaɓe.

Hakazalika, ya yabawa Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, bisa kafa Kwamitin Kartakwana kan Rajistar Katin Zaɓe (CVR), yana mai cewa wannan shiri zai taimaka matuƙa wajen ƙara wayar da kan al’umma da ƙarfafa tubalan dimokuraɗiyya a Jihar Kano.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rushe Tsarin Karatu Mai Dauke Da JSS Da SS A Makarantun Sikandire A Najeriya

June 30, 2026

Jami’ar Northwest Kano Ta Kori Dalibai 34 Saboda Karya Dokokin Jarabawa ‎

June 30, 2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 2026

NDLEA Ta Kone Tan 12.2 Na Miyagun Ƙwayoyi a Kano, Ta Kama Mutum 

June 29, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.