Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman
Afrika

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Shugaban Karamar Hukumar Dala Ya Yi Kira Ga Masu Hannu Da Shuni Su Tallafawa Yunkurin Gwamnati Don Bunkasa Ilimi Da Lafiya

Shugaban karamar hukumar Dala, Alhaji Surajo Ibrahim Imam, ya yi kira ga masu hannu da shuni da kamfanoni su tallafawa yunkurin gwamnati na bunkasa ilimi da lafiyar al’umma. Ya bayyana hakan ne yayin bikin bude dakunan gwajin kimiyya (laboratories) a makarantar mata ta GGC Dala, wanda aka gudanar tare da halartar Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Sanusi Lamido Sanusi II.

Dakunan gwajin da aka kaddamar sun hada da:

Chemistry Laboratory mai suna Gwamna Eng. Abba Kabir Yusuf,

Physics Laboratory mai suna Mai Martaba Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi,

Biology Laboratory mai suna A.B. Mahmud SAN,

Agricultural Laboratory mai suna Alhaji Umar Haruna Doguwa.

Wannan aiki ya samu tallafi daga wani babban kamfanin sadarwa wanda ya dauki nauyin samar da wadannan dakunan zamani. Shugaban karamar hukumar, Alhaji Surajo Imam, ya yaba wa kokarin kamfanin, tare da godewa hamshakin attajirin nan, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, wanda ya bayar da gudummawar kudi da aka yi amfani da su wajen sayen kayan aiki na asibitoci domin bunkasa kiwon lafiyar al’umma.

A jawabinsa, Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Sanusi Lamido Sanusi II, ya bayyana jin dadinsa bisa wannan ci gaba, yana mai bayyana makarantar GGC Dala a matsayin makaranta mai tarihi wacce aka kafa tun shekaru 64 da suka wuce. Sarkin ya kuma yabawa kokarin daliban makarantar wajen karatun Alkur’ani mai tsarki, tare da kira ga kamfanoni su ci gaba da tallafawa bangaren ilimin kimiyya a Najeriya.

Wakilin kwamishinan ilimi na jihar Kano, Dr. Ali Haruna Makoda, wanda sakataren ma’aikatar ilimi ya wakilta, ya yaba wa wannan kokari, tare da godewa Sarkin Kano da kamfanin sadarwa bisa wannan gudunmawa.

Shugaban makarantar GGC Dala, Hajiya Ramatu Muktar Tofa, ta jinjina wa wadanda ke tallafawa makarantar, ciki har da Alhaji Aminu Dantata, kungiyar tsofaffin daliban makarantar karkashin Hajiya Saudatu Sani, da kuma kungiyar iyaye da malamai karkashin Alhaji Ado Muktar Adnan. Ta kuma gode wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na farfado da harkar ilimi a jihar Musamman

Taron ya samu halartar manyan baki da suka hada da Hakimai, shugabannin unguwanni, shugaban jam’iyyar NNPP na Dala, kansiloli, da masu ba da shawara ga shugaban karamar hukumar.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.