Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman
Afrika

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Shugaban Karamar Hukumar Dala Ya Yi Kira Ga Masu Hannu Da Shuni Su Tallafawa Yunkurin Gwamnati Don Bunkasa Ilimi Da Lafiya

Shugaban karamar hukumar Dala, Alhaji Surajo Ibrahim Imam, ya yi kira ga masu hannu da shuni da kamfanoni su tallafawa yunkurin gwamnati na bunkasa ilimi da lafiyar al’umma. Ya bayyana hakan ne yayin bikin bude dakunan gwajin kimiyya (laboratories) a makarantar mata ta GGC Dala, wanda aka gudanar tare da halartar Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Sanusi Lamido Sanusi II.

Dakunan gwajin da aka kaddamar sun hada da:

Chemistry Laboratory mai suna Gwamna Eng. Abba Kabir Yusuf,

Physics Laboratory mai suna Mai Martaba Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi,

Biology Laboratory mai suna A.B. Mahmud SAN,

Agricultural Laboratory mai suna Alhaji Umar Haruna Doguwa.

Wannan aiki ya samu tallafi daga wani babban kamfanin sadarwa wanda ya dauki nauyin samar da wadannan dakunan zamani. Shugaban karamar hukumar, Alhaji Surajo Imam, ya yaba wa kokarin kamfanin, tare da godewa hamshakin attajirin nan, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, wanda ya bayar da gudummawar kudi da aka yi amfani da su wajen sayen kayan aiki na asibitoci domin bunkasa kiwon lafiyar al’umma.

A jawabinsa, Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Sanusi Lamido Sanusi II, ya bayyana jin dadinsa bisa wannan ci gaba, yana mai bayyana makarantar GGC Dala a matsayin makaranta mai tarihi wacce aka kafa tun shekaru 64 da suka wuce. Sarkin ya kuma yabawa kokarin daliban makarantar wajen karatun Alkur’ani mai tsarki, tare da kira ga kamfanoni su ci gaba da tallafawa bangaren ilimin kimiyya a Najeriya.

Wakilin kwamishinan ilimi na jihar Kano, Dr. Ali Haruna Makoda, wanda sakataren ma’aikatar ilimi ya wakilta, ya yaba wa wannan kokari, tare da godewa Sarkin Kano da kamfanin sadarwa bisa wannan gudunmawa.

Shugaban makarantar GGC Dala, Hajiya Ramatu Muktar Tofa, ta jinjina wa wadanda ke tallafawa makarantar, ciki har da Alhaji Aminu Dantata, kungiyar tsofaffin daliban makarantar karkashin Hajiya Saudatu Sani, da kuma kungiyar iyaye da malamai karkashin Alhaji Ado Muktar Adnan. Ta kuma gode wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na farfado da harkar ilimi a jihar Musamman

Taron ya samu halartar manyan baki da suka hada da Hakimai, shugabannin unguwanni, shugaban jam’iyyar NNPP na Dala, kansiloli, da masu ba da shawara ga shugaban karamar hukumar.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026

NAPTIP Ta Ceto Mata Bakwai Ake Zargin Ana Shirin Safarar Su zuwa Ƙasar Iraki A Kano ‎

February 12, 2026

Tirela Ta Murkushe Mutum Biyu Har Lahira A kaduna  ‎

February 12, 2026

Mata sun fi maza yin aikin baban-giwa a Najeriya

February 11, 2026

Dalilin Da Ya Sa Na Ajiye Shugabancin NAHCON – Abdullahi Saleh Pakistan

February 11, 2026

Jihar Abia Ta Sanya Hannu Kan Dokar Tallafin Tsofaffi

February 9, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

By WafsymFebruary 12, 2026

A daidai lokacin da ya rage ‘yan kwanaki kaɗan a shiga watan Ramadan mai alfarma,…

‎“Ya Kamata ‘Yan Jaridu Su Riƙa Nuna Tausayi, Hikima Da Mutunta Jinƙan Ɗan Adam wajen ɗauko labarai ‎ ‎ ‎—Comrade Abbas Ibrahim

January 21, 2026

‎Kisan Gilla: Shawarwari Ga Mata Masu Zaman Gida Don Kare Rayukansu

January 19, 2026

‎Sauyin Yanayi Na Canza Yanayin Sanyi A Arewacin Najeriya  ‎ ‎ ‎— Masana ‎

January 18, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.