Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Mun amince da ficewar Mali da Nijar da kuma Burkina Faso – ECOWAS
Afrika

Mun amince da ficewar Mali da Nijar da kuma Burkina Faso – ECOWAS

December 16, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen Afrika ta ECOWAS ta amince da ficewar Mali da Nijar da kuma Burkina Faso daga cikinta.

Ƙungiyar ta ɗauki matakin ne a babban taron ta na ƙoli da shugabannin ƙungiyar suka gudanar a Abuja.

Jagororin ƙungiyar ta ECOWAS ko CEDEAO ɗin sun nuna amincewa da buƙatar da ƙasashen uku suka miƙa musu na janyewa daga ƙungiyar daga ranar 29 ga watan Janairu na 2025 da ke tafe.

Haka kuma shugabannin ƙungiyar sun amince da naɗa shugaban Togo da na Senegal domin su cigaba da tattauna wa da ƙasashen Mali da Nijar da Burkina Faso har zuwa cikar wa’adin da nufin ba su haƙuri ko zasu aminta su sauya matsaya domin komawa cikin ƙungiyar.

Haka kuma ƙungiyar ta ECOWAS a zaman da ta yi a ranar Lahadi 15 ga Disamba ta amince a kafa wata kotu ta musamman domin yin hukunci dangane da laifukan da aka aikata a lokacin mulkin tsohon shugaban ƙasar Gambia Yahya Jammeh.

Ƙasashen na Mali da Burkina Faso da Nijar ba su tura ko da wakili ɗaya a yayin taron da aka gudanar a Abuja ba.

Sai dai a ranar Juma’a shugabannin ƙashen uku sun yi taron nasu a Yamai babban birnin Nijar inda a nan ne ma suka jaddada cewa “ba za su koma ƙungiyar ECOWAS ba”.

Bayan kasashen Burkina Faso da Mali da Nijar sun bayyana matakin ficewa daga kungiyar, ECOWAS ta nada shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye a matsayin mai shiga tsakani da zai jagoranci tattaunawa da kasashen uku da suka kafa Sahel Alliance.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yawan Al’umma Na Iya Tsananta Matsalar Tsaro a Nijeriya-Bankin Duniya

October 20, 2025

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.