Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » NAPTIP ta kama mutane biyar da ake zargi da safarar mutane
Afrika

NAPTIP ta kama mutane biyar da ake zargi da safarar mutane

October 2, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
naptip

Hukumar Yaƙi da Safarar Mutane ta Najeriya (NAPTIP) ta bayyana cewa ta cafke mutum biyar da ake zargi da hannu a safarar mutane tare da kuɓutar da mutum 24 a filin jirgin sama na kasa da kasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Vincent Adekoye, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, inda ya ce cikin waɗanda aka kama har da wani mutum da ya yi ƙoƙarin safarar ‘yarsa zuwa ƙasar Iraƙi.

Jami’in Ɗan Sanda Ya Harbe Kansa Da Bindiga Bisa Kuskure A Kano

Wannan samame ya biyo bayan bayanan sirri ne da hukumar ta samu, kuma an gudanar da shi ƙarƙashin jagorancin Babbar Daraktar NAPTIP, Binta Adamu Bello.

Adekoye ya ce cikin waɗanda aka kama akwai wani babban jami’in tsaro da ake zargi da kasancewa cikin ƙungiyar masu safarar mutane a yankin kudu maso yamma na ƙasar.

> “Mun kuɓutar da yara da matasa masu shekaru tsakanin 15 da 26, waɗanda aka ɗauko daga jihohin Kano, Katsina, Oyo, Ondo da Ribas, kuma suna kan hanyarsu ta zuwa ƙasashen Iraƙi, Sudan, Masar, Saudiyya, Bahrain da Afghanistan,” in ji shi.

Adekoye ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka kuɓutar ta bayyana cewa za ta tabbatar da an gurfanar da mahaifinta a kotu kan yunƙurin safararta da ya yi zuwa Iraƙi.

Haka kuma, wata daga cikin waɗanda aka yi ƙoƙarin safarar ta ce mahaifiyarta ce ta tilasta mata ta amince da tafiya zuwa Turai domin yin aiki da za ta rika samun daloli.

Hukumar NAPTIP ta jaddada cewa za ta ci gaba da kai sama-samar da ayyuka na musamman tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro domin ƙarfafa yaƙi da safarar mutane da kuma tabbatar da cewa duk wanda aka kama da hannu a irin wannan laifi ya fuskanci hukunci.

abuja Featured naptip
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yawan Al’umma Na Iya Tsananta Matsalar Tsaro a Nijeriya-Bankin Duniya

October 20, 2025

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.