Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » NDLEA da NAPTIP Zasu Ƙarfafa Haɗin Gwiwa don Yaƙi da Safarar Miyagun Kwayoyi da Mutane
Afrika

NDLEA da NAPTIP Zasu Ƙarfafa Haɗin Gwiwa don Yaƙi da Safarar Miyagun Kwayoyi da Mutane

April 25, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
NDLEA LOGO

Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) tare da Hukumar Hana Fataucin Mutane (NAPTIP) sun kafa wata rundunar jami’an su domin hada karfi tare wajen yaƙi da safarar miyagun kwayoyi da safarar mutane.

Wannan mataki ya fito ne a lokacin da Shugabar NAPTIP, Binta Lami Adamu Bello, ta kai ziyarar girmamawa ga Shugaban NDLEA, na Kasa Birgediya Janar Mohammed Buba Marwa, mai ritaya a hedikwatar NDLEA dake Abuja, yau jumma’a 25 ga Afrilu, 2025.

A cikin jawabinsa, Marwa ya taya Binta Adamu Bello, murna bisa nadinta da shugaban Kasa Bola Ahamad Tunibu,yayi kuma ya yaba da yadda ta soma aiki da ƙwazo.
Ta cikin wata sanarwa da daraktan Yaɗa labarai da wayar daa kan jamma’a a hukumar Femi Baba Femi,Yafitar Ya bayyana cewa akwai alaƙa tsakanin safarar mutane da safarar miyagun kwayoyi, inda wasu daga cikin waɗanda ake safararsu ke zama masu ɗaukar kwayoyi ba tare da saninsu ba.
Sanarwar ta kara da cewa akwai bukatar haɗin gwiwa ta hanyar sanya hannu kan yarjejeniya (MoU) da za ta fayyace fannoni na aiki tare.

A nata bangaren, Shugabar yaki da safarar mutane da cin zarafin kananan Yara NAPTIP ta Kasa Binta Lami Adamu Bello, ta bayyana cewa akwai buƙatar haɗin kai sosai tsakanin hukumomin biyu domin toshe hanyoyin aikata laifukan, musamman ganin yadda ammfani da kananan Yara da Mata wajen safarar kwayoyi, sannan a kan yi musu allura ko a basu kwayoyi domin su kasance masu biyayya.

Ta kuma jaddada cewa laifukan biyu nafaruwa ne a iyakoki marasa tsaro, rashawa, talauci, da raunin hukumomi. Ta ce akwai buƙatar gina tsarin aiki na haɗin gwiwa wanda zai haɗa da bincike da musayar bayanan sirri, horas da ma’aikata tare, amfani da fasaha da bayanai, wayar da kai ga jama’a, da kuma yin garambawul ga dokoki.

Hukumomin sun amince da kafa shirin aiki na NDLEA da NAPTIP na lokaci gajere zuwa matsakaici, da gudanar da taron duba ayyuka sau ɗaya ko biyu a shekara, da kuma inganta haɗin gwiwa da ƙungiyoyi na ƙasa da ƙasa.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yawan Al’umma Na Iya Tsananta Matsalar Tsaro a Nijeriya-Bankin Duniya

October 20, 2025

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.