Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Karamar hukumar Minjibir a nan Kano zatayi dokar da zata hukunta, masu fadan daba da kilisa
Afrika

Karamar hukumar Minjibir a nan Kano zatayi dokar da zata hukunta, masu fadan daba da kilisa

April 22, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Minjibir

Majalisar karamar hukumar Minjibir a nan Kano zatayi dokar da zata hukunta, masu fadan Daba kilisa,da Kidan a fanin karamar hukumar sakamakon matsalolin da suke haifarwa.

Shugaban karamar hukumar ta Minjibir Kaftin Jibrin Na lado Kunya,ne ya bayana hakan yayin wani taron masu ruwa da tsaki a karamar hukumar da Kungiyar Minjibir Solidarity Forum ta shirya dan kara kawo cigaba a karamar hukumar dama jihar Kano baki daya.

Kaftin Jibrin Na lado Kunya Ya kara da cewar “yanzu haka majalisar karamar hukumar ta Minjibir ta kamala tataunawa da masu ruwa da tsaki musamman a fanin tsaro da zamantakewa dan samar da dokar Wanda zatayi tanadi kan irin hukuncin da masu fadan Daba, Kidan Dije da kuma masu kilisa zasu fuskanta matukar suka sabawa dokar”shugaban karamar hukumar Minjibir.

A nasa jawabin Tun da fari tsohon shugaban kungiyar kwadago ta kasa reshen jihar Kano kuma mataimakin shugaban kungiyar ta kasa Kwamared Kabiru Ado Minjibir cewa yayi “Sai an samar dokar da zata sahalewa duk Wanda zai yi Kilisa ko kidan Dije dan samar da mafita ga abubuwan dake biyo baya na fadan Daba Tsakanin matasan karamar hukumar domin bai kamata a zubawa lamarin idanu yana jawo asarar dukiya da jikkata Al’umma ba Amma samar dokar da tsarin da masu kilisa ko kidan DJ zasu bi bayan Neman izzini zai sa Wanda suka shirya irin wannan taruka su tabbatar da ganin cewa ba a samu karya doka ko cin zarafin mutane ba”Cewar Mataimakin shugaban kungiyar kwadago ta Kasa Kabiru Ado Minjibir.

Da yake nasa jawabin shugaban kungiyar ta Minjibir Solderity Forum, ya ce “Makkasudin taron shi ne samar da hadinkai da kuma kawo Ayukan cigaba karamar hukumar Kamar Hanyoyi, Samarwa matasa ayukan yi da kuma Ilimin sai ababen more rayuwa.

Wakilinmu ya rawaito cewa taron ya samu halartar mutane yan asalin karamar hukumar ta Minjibir da sukayi fice a fanin siyasa,aikin Gwamnatin da kasuwanci da kuma masu bawa karamar hukumar gudunmawar da ta kama a fanin da suke da kwarewa.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yawan Al’umma Na Iya Tsananta Matsalar Tsaro a Nijeriya-Bankin Duniya

October 20, 2025

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.