Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano
Afrika

Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano

January 12, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
FB IMG 1768137049373

Bayan shafe wasu makonni ana fama da zafi mai tsanani, birnin Kano ya sake fuskantar yanayin sanyi mai ƙarfi tare da ƙura da hazo, abin da ke nuna shigowar lokacin hunturu.

‎Sauyin yanayin ya fara ne a ƙarshen makon da ya gabata, inda mutane da dama suka fara jin tasirinsa a rayuwarsu ta yau da kullum. Wasu mazauna birnin na cewa irin wannan yanayi na nuna yadda sauyin yanayi ke ƙara bayyana a Arewa cikin ‘yan shekarun nan.

Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Kuɗin 2026 Na Naira Tiriliyan 4.4

‎Wakilinmu ya tattauna da wasu mazauna Kano domin jin ra’ayoyinsu kan yadda wannan yanayi ke shafar kasuwanci, zirga-zirga da lafiyar jama’a.

‎Rukayya Ibrahim daga Goron Dutse ta ce yanayin bana ya bambanta da na shekarun baya.

‎“A ganin nawa, hakan na da alaƙa da ƙarancin ruwan sama a bara. Idan ruwan sama ya yi yawa, sanyi yakan fi tsanani,” in ji ta.

‎Sai dai ta ce wannan yanayi na kawo cikas ga kasuwancinta na sayar da kayan sha masu sanyi.

‎“Idan sanyi ya yi yawa, mutane ba sa saya. Ni na fi samun riba idan rana na da zafi,” ta ƙara da cewa.

‎A nata ɓangaren, Hafiz Umar, ɗan kasuwa a Kantin Kwari, ya ce sanyi yana rage zafin kasuwa, amma ƙura na kawo matsala.

‎“Sanyi yana sauƙaƙa harkokin kasuwa, amma ƙurar hazo na kawo mura da tari, sannan tana iya lalata kaya,” in ji shi.

‎Wasu mazauna Kano sun ce sun riga sun fara jin tasirin wannan yanayi a lafiyarsu.

‎Bilkisu Ibrahim daga Sabuwar Gandu ta ce ta kamu da mura da zazzabi sakamakon canjin yanayi.

‎“Yanzu dole in rika kula sosai, musamman da ruwan da nake amfani da shi,” in ji ta.

‎A gefe guda kuma, wasu na ganin sanyi a matsayin alheri, musamman ganin watan Ramadan na gabatowa.

‎

‎Ibrahim Shehu ya ce:

‎“Idan wannan yanayi ya ci gaba har lokacin azumi, hakan zai rage wahalar zafi.”

‎

‎Komawar sanyi da hazo a Kano ya jawo ra’ayoyi mabambanta daga jama’a. Yayin da wasu ke jin daɗin sauƙin yanayi, wasu kuma na fuskantar ƙalubale a kasuwanci da lafiya. Masana dai na danganta irin wannan canji da matsalar sauyin yanayi da ke ƙara bayyana a duniya.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rushe Tsarin Karatu Mai Dauke Da JSS Da SS A Makarantun Sikandire A Najeriya

June 30, 2026

Jami’ar Northwest Kano Ta Kori Dalibai 34 Saboda Karya Dokokin Jarabawa ‎

June 30, 2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 2026

NDLEA Ta Kone Tan 12.2 Na Miyagun Ƙwayoyi a Kano, Ta Kama Mutum 

June 29, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.