Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano
Afrika

Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano

January 12, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
FB IMG 1768137049373

Bayan shafe wasu makonni ana fama da zafi mai tsanani, birnin Kano ya sake fuskantar yanayin sanyi mai ƙarfi tare da ƙura da hazo, abin da ke nuna shigowar lokacin hunturu.

‎Sauyin yanayin ya fara ne a ƙarshen makon da ya gabata, inda mutane da dama suka fara jin tasirinsa a rayuwarsu ta yau da kullum. Wasu mazauna birnin na cewa irin wannan yanayi na nuna yadda sauyin yanayi ke ƙara bayyana a Arewa cikin ‘yan shekarun nan.

Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Kuɗin 2026 Na Naira Tiriliyan 4.4

‎Wakilinmu ya tattauna da wasu mazauna Kano domin jin ra’ayoyinsu kan yadda wannan yanayi ke shafar kasuwanci, zirga-zirga da lafiyar jama’a.

‎Rukayya Ibrahim daga Goron Dutse ta ce yanayin bana ya bambanta da na shekarun baya.

‎“A ganin nawa, hakan na da alaƙa da ƙarancin ruwan sama a bara. Idan ruwan sama ya yi yawa, sanyi yakan fi tsanani,” in ji ta.

‎Sai dai ta ce wannan yanayi na kawo cikas ga kasuwancinta na sayar da kayan sha masu sanyi.

‎“Idan sanyi ya yi yawa, mutane ba sa saya. Ni na fi samun riba idan rana na da zafi,” ta ƙara da cewa.

‎A nata ɓangaren, Hafiz Umar, ɗan kasuwa a Kantin Kwari, ya ce sanyi yana rage zafin kasuwa, amma ƙura na kawo matsala.

‎“Sanyi yana sauƙaƙa harkokin kasuwa, amma ƙurar hazo na kawo mura da tari, sannan tana iya lalata kaya,” in ji shi.

‎Wasu mazauna Kano sun ce sun riga sun fara jin tasirin wannan yanayi a lafiyarsu.

‎Bilkisu Ibrahim daga Sabuwar Gandu ta ce ta kamu da mura da zazzabi sakamakon canjin yanayi.

‎“Yanzu dole in rika kula sosai, musamman da ruwan da nake amfani da shi,” in ji ta.

‎A gefe guda kuma, wasu na ganin sanyi a matsayin alheri, musamman ganin watan Ramadan na gabatowa.

‎

‎Ibrahim Shehu ya ce:

‎“Idan wannan yanayi ya ci gaba har lokacin azumi, hakan zai rage wahalar zafi.”

‎

‎Komawar sanyi da hazo a Kano ya jawo ra’ayoyi mabambanta daga jama’a. Yayin da wasu ke jin daɗin sauƙin yanayi, wasu kuma na fuskantar ƙalubale a kasuwanci da lafiya. Masana dai na danganta irin wannan canji da matsalar sauyin yanayi da ke ƙara bayyana a duniya.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026

NAPTIP Ta Ceto Mata Bakwai Ake Zargin Ana Shirin Safarar Su zuwa Ƙasar Iraki A Kano ‎

February 12, 2026

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf A Matsayin Shugaban NAHCON

February 11, 2026

Mata sun fi maza yin aikin baban-giwa a Najeriya

February 11, 2026

Dalilin Da Ya Sa Na Ajiye Shugabancin NAHCON – Abdullahi Saleh Pakistan

February 11, 2026

Jihar Abia Ta Sanya Hannu Kan Dokar Tallafin Tsofaffi

February 9, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

By WafsymFebruary 12, 2026

A daidai lokacin da ya rage ‘yan kwanaki kaɗan a shiga watan Ramadan mai alfarma,…

‎“Ya Kamata ‘Yan Jaridu Su Riƙa Nuna Tausayi, Hikima Da Mutunta Jinƙan Ɗan Adam wajen ɗauko labarai ‎ ‎ ‎—Comrade Abbas Ibrahim

January 21, 2026

‎Kisan Gilla: Shawarwari Ga Mata Masu Zaman Gida Don Kare Rayukansu

January 19, 2026

‎Sauyin Yanayi Na Canza Yanayin Sanyi A Arewacin Najeriya  ‎ ‎ ‎— Masana ‎

January 18, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.