Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Ƙungiyar ɗaliban makarantar FGC ta Kano sun kai ƙara gurin Tinubu bisa zargin yunƙurin wawashe filin makarantar
Afrika

Ƙungiyar ɗaliban makarantar FGC ta Kano sun kai ƙara gurin Tinubu bisa zargin yunƙurin wawashe filin makarantar

April 6, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
FB IMG 1775434603827

Kungiyar tsoffin daliban makarantar FGC ta Kano, mai suna FGCKOSA ta aike da ƙorafi ga shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu bisa abinda ta kira da wawashe katafaren filin makarantar.

Daily Nigerian Hausa ta gano cewa ma’aikatar ilimi ta ƙasa da haɗin gwiwar wani kamfani, Pluck Global Company Ltd. sun kulla yarjejeniyar yanka wa da yin gine-gine a filin, wanda a ke sa ran gobe Litinin za a ƙaddamar da aikin a harabar makarantar .

Shugaba Tinubu ya amince da biyan bashin ₦3.3tn don inganta wutar lantarki

Takardar korafin ta samu saka hannu na haɗin gwiwa da shugaban ƙungiyar na duniya, Shoyinka Shodunke da kuma wasu shahararrun mambobin ta da su ka haɗa da Sheikh Bashir Umar Aliyu, shugaban majalisar ƙoli ta shari’a ta kasa da Sheikh Rabiu Ishyaku Rabiu, shugaban rukunin kamfanin IRS.

Sauran da su ka rattaba hannu a takardar korafin sun haɗa da Engr. Suleiman Adamu, Galadiman Kazure, ⁠Alhaji Nasser Ahmed Dan Darman Lokoja da kuma ⁠Abdul Samaad Rabiu, shugaban rukunin kamfanonin BUA.

An kuma aike kwafin ta ga shugaban majalisar dattawa, shugaban majalisar wakilai da ministan ilimi da ƙaramin ministan ilimi da hukumomin ICRC, EFCC da ICPC, ƙungiyar ta ce sam ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa.

A cewar Shokunde, ƙungiyar ta samu labarin cewa ana kokarin handame filin wanda ya ƙunshi filayen wasanni da masallaci da sauran gine-gine masu muhimmanci a makarantar.

Ya kara da cewa ana shirin karbe filin makarantar ba tare da wata tuntuba ba, inda ya ce kamata ya yi ma a karawa FGC din girma na wai a rika rage ta na.

A cewar sa, FGCKOSA ta shafe sama da shekaru 30 tana kashe biliyoyin naira wajen cigaban makarantar ba tare da sa ran samun wata riba ta kuɗi ba.

“Har wata gidauniya muka bude mai suna FGCKOSA Foundation ba dan komai ba sai dan mu taimaka wajen cigaban FGC.

” A yanzu haka muna shirin sake tara biliyoyin naira domin mun cigaba da dorar da kokarin cigaban FGC, amma sai gashi mun samu wani mummunan labari.

“To ba za mu yarda da wannan ba. Za mu yi duk me yuwuwa mu dakile wannan yunkuri,” in ji Shokunde.

A karon gayyatar zuwa bikin ƙaddamar da aikin a filin da Daily Nigerian Hausa ta samu kwafi, Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ne babban bako a taron, sai kuma Kwamishinan Ƙasa, Abduljabbar Garko a matsayin babban mai jawabi sai kuma dattijon jam’iyyar APC na ƙasa, Mohammed Jamu Yusuf a matsayin mai jawabi ma biyu.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Allah Ya yi wa Alhaji Sani Gwarzo, wanda aka fi sani da “Tumbuleke”, rasuwa.

August 11, 2026

Babu Mafaka Ga Masu Safarar Miyagun Ƙwayoyi A Kano — Muhyi Magaji

August 11, 2026

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.