Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump
Babban Labari

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
709995 750x375

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa yana bukatar a saka Amurka cikin tsarin zaben sabon shugaban Iran.

Trump ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da kafar yada labarai ta Axios ranar Alhamis, kwanaki biyar bayan kashe jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, a wani hari da Amurka da Isra’ila suka kai kan gidansa a Tehran.

Majalisar Dokokin Kano ta fara yunƙurin tsige mataimakin Gwamna

A cewar Trump, Iran na bata lokacinta idan ta yi kokarin nada sabon jagora ba tare da sa hannun Amurka ba.

Ya kuma bayyana cewa Mojtaba Khamenei, ɗan marigayi Ali Khamenei wanda ake ganin zai iya gaje shi, ba zabin da zai amince da shi ba.

Trump ya bayyana shi a matsayin mutum mara karfi, yana mai cewa:

“Dan Khamenei ba zabin da zan amince da shi ba. Muna son wanda zai kawo zaman lafiya da hadin kai a Iran.”

Ya kara da cewa dole ne shi kansa ya shiga cikin tsarin zaben sabon shugaban, yana mai kwatanta lamarin da yadda Amurka ta shiga cikin sauyin shugabanci a Venezuela.

Trump ya kuma ce ba zai amince da duk wani sabon shugaban Iran da zai ci gaba da manufofin gwamnatin da ta gabata ba.

A cewarsa, idan hakan ta faru, za a iya sake samun rikici tsakanin Amurka da Iran cikin shekaru biyar masu zuwa.

Tun da farko, Trump ya ce mafi munin sakamakon yakin da ake yi yanzu shi ne idan wani shugaba mai tsattsauran ra’ayi kamar marigayi Khamenei ya karbi mulki.

Ya kuma bayyana cewa wasu daga cikin mutanen da Amurka ta yi tunanin za su iya jagorantar Iran sun mutu a hare-haren farko da aka kai.

Kalaman Trump na zuwa ne yayin da yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran ke ci gaba, inda rahotanni suka nuna cewa sama da Iraniyawa 1,000 sun mutu, yayin da sojojin Amurka shida da mutane 11 a Isra’ila suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren Iran.zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump.

 

Premium times

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim

April 29, 2026

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026

An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje

April 24, 2026

El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi

April 21, 2026

Dole Najeriya ta samu tsaro – Babban hafsan tsaro

April 20, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.