Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Majalisar Dokokin Kano ta fara yunƙurin tsige mataimakin Gwamna
Babban Labari

Majalisar Dokokin Kano ta fara yunƙurin tsige mataimakin Gwamna

March 6, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
25489720 1884 11f1 aff7 a32b6621d3cc.jpg

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta fara shirin tsige mataimakin gwamnan jihar, kwamared Aminu Abdulsalam, bisa zarge-zargen aikata manyan laifuka a kan aiki, wulaƙanta aiki da kuma karya dokokin aikin gwamnati.

Matakin ya biyo bayan wani ƙorafi da ɓangaren zartarwa ya gabatar wa majalisar, inda aka buƙaci ta ɗauki mataki a kan Abdulsalam kan wasu zarge-zargen da suka shafi yadda ya gudanar da aikinsa a lokacin da yake kwamishinan ƙananan hukumomi tsakanin shekarar 2023 zuwa 2024.

Gwamnatin Jigawa Ta Tsige Alƙalin Kotun Musulunci Kan Rashawa

Da yake karanta ƙorafin, Shugaban nasu rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini Dala, ya ce sanarwar ta yi daidai da tanadin sashe na 188 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima). Ya bayyana cewa zarge-zargen sun shafi ayyukan Abdulsalam ne a lokacin da yake kula da ƙananan hukumomi 44 na jihar.

 

Ƙorafin ya ƙunshi zarge-zarge kamar haka: Cin amanar al’umma da keta haddin aiki.

 

Ana zargin Abdulsalam da karkatar da kuɗaɗen da aka ware wa ƙananan hukumomi domin amfanin kansa. Daga watan Yuni 2023 zuwa Janairu 2024, ana zargin ya karɓi kuɗaɗen cin hanci har naira miliyan ₦462 a cikin watanni bakwai.

 

Karkatar da Kuɗaɗe da amfani da muƙami ta hanyar da ba ta dace ba: Daga watan Fabrairu 2024 zuwa Yuli 2024, an ce ya karɓi kimanin Miliyan ₦726 daga ƙananan hukumomi da sunan aiwatar da wasu ayyuka na musamman.

 

Amfani da ofis ta hanyar da ba ta dace ba:

 

Ana kuma zargin Abdulsalam da taimakawa wajen sakin kuɗi har ₦440 miliyan ga kamfanin North Med Pharmaceutical Limited, wanda ake cewa ya saɓa dokokin sayen kayayyakin gwamnati da kuma ƙa’idojin kashe kuɗin jihar.

 

Babban laifi a kan aiki:

 

An ce waɗannan ayyuka sun kai matsayin manyan laifuka a kan aiki kamar yadda sashe na 188(2) na kundin tsarin mulki ya tanada, domin suna nuna karya dokokin tsarin mulki da ƙa’idojin da suka shafi masu riƙe da muƙaman gwamnati.

 

Dala ya bayyana cewa bisa hujjojin da aka gabatar, ya kamata a tsige mataimakin gwamnan tare da cire shi daga muƙaminsa bisa tsarin da kundin tsarin mulki ya tanada.

 

Sai dai an bai wa Abdulsalam wa’adin makonni biyu domin ya mayar da martani kan zarge-zargen da ke ƙunshe cikin ƙorafin.

 

Rahotanni na nuni da cewa batun ƙin canja jam’iyya daga NNPP zuwa APC shi ma yana daga cikin dalilan da ake kawowa na yunƙurin tsige mataimakin gwamna, ko a kwanakin baya an dinga yaɗa wa cewa majalisar za ta tsige shi, wanda a wancan lokacin majalisar dokoki ta musanta zargin, wanda a yau kuma sai ga batun tsigewar ya fito.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim

April 29, 2026

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026

An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje

April 24, 2026

El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi

April 21, 2026

Dole Najeriya ta samu tsaro – Babban hafsan tsaro

April 20, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.