Mai martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sunusi na II, ya bukaci gwamnatin jihar Kano da ta dauki tsauraran matakai wajen hukunta duk wanda aka samu da hannu a kisan gilla, musamman kan mutanen da ba su aikata wani laifi ba.
Sarkin ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai, inda ya yi tsokaci kan kisan gillar da wasu ɓata-gari suka aikata wa Fatima Abubakar da ’ya’yanta shida a yankin Chiranci Dorayi Gidan Kwari da ke karamar hukumar Kumbotso, a karshen makon da ya gabata.
Kisan Gilla: Shawarwari Ga Mata Masu Zaman Gida Don Kare Rayukansu
Khalifa Muhammadu Sunusi na II ya ce gazawar hukunta masu aikata irin wadannan laifuka yadda ya kamata na kara yawaitar aikata su a cikin al’umma. A cewarsa, “Idan aka bar wanda ya kashe wani ba tare da an hukunta shi ba, to hakan na nufin kisan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba, ba zai taba karewa ba.”
Sarkin ya kuma yi addu’ar Allah Ya jikansu, tare da bai wa iyalansu da daukacin al’ummar Musulmi hakurin jure wannan babban rashi.
Haka kuma, ya yi kira ga al’umma da su kasance masu sa ido, tare da gaggauta sanar da jami’an tsaro mafi kusa da su duk lokacin da suka lura da wani abu da ba su yarda da shi ba, domin dakile aikata laifuka kafin su afku.

