Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » FA ta dakatar da Mudryk daga buga kwallo – Barcelona ta dauki dan kasar Mali Ibrahim Diarra (17) daga Academia África Foot – FAGEN WASANNI
Wasanni

FA ta dakatar da Mudryk daga buga kwallo – Barcelona ta dauki dan kasar Mali Ibrahim Diarra (17) daga Academia África Foot – FAGEN WASANNI

December 17, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2024 12 17 at 13.09.15
WhatsApp Image 2024 12 17 at 13.09.15

Hukumar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Ingila ta dakatar da ɗan wasan Chelsea Mykhailo Mudryk daga buga wasa zuwa wani ɗan lokaci, bisa zarginsa da ta’ammali da ƙwayoyi.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea ta tabbatar da hukumar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Ingila ta tuntuɓeta akan dan wasanta Mykhailo Mudryk game da zargin da ake yi masa na yin amfani da ƙwayoyi ba bisa ka’ida ba.

Hukumar ta Gano Hakan ne bayan gwajin fitsari da aka yi masa tare da wasu ƴan wasa.

“Dukkan kungiyar mu har da Mykhailo Mudryk muna ba da cikakken goyon baya ga hukumar kwallon kafa ta Ingila (FA) akan gwajin da take yi akai-akai, har da Mykhailo Mudryk.

“Mykhailo ya tabbatar da cewa bai taɓa amfani da wasu haramtattun kwayoyi da gangan ba.

A halin yanzu, Mykhailo tare da mu zamu yi aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin da abun ya shafa domin gano bakin zaren al’amarin da ya haifar da wannan sakamakon. Ba zamu kara tsokaci akai ba.” Inji Chelsea

Kungiyoyin Bayern Munich da Real Madrid da Manchester City sun cire rai a farautar ɗan wasan Jamus mai shekara 21, Florian Wirtz, bayan Bayer Leverkusen ta shirya tsawaita kwantiraginsa har zuwa 2028.

Manchester United ta sa ɗan wasanta na Ingila Marcus Rashford, mai shekara 27 a kasuwa kuma za ta amince da zabtare farashinsa a watan Janairu.

Ɗan wasan gaba a Liverpool da Masar Mohamed Salah, mai shekara 32, na dab da sa hannu a sabuwar yarjejeniyar tsawaita zamansa da ƙungiyar.

Barcelona ta dauki dan wasan tsakiyar kasar Mali Ibrahim Diarra me shekaru (17) daga Academia África Foot akan kwantiragi har zuwa 30 ga Yuni, 2028.

Kawo zuwa yanzu yan wasan da suka fi yawan zura kwallaye a Firimiya lig:

Erling Haaland – 13

Mohamed Salah – 13

Cole Palmer – 11

Bryan Mbeumo – 10

 

Wasu kafafen watsa labarai a Morocco na ta suka gami da nuna rashin jin dadinsu bayan da CAF ta bayyana Ademola Lookman a matsayin gwarzon dan wasan nahiyar Afirka na wannan shekarar.

Tun a daren jiya wajen bayar da kyautar, aka fara hango wasu fuskoki suna fita waje bayan an bayyana Ademola Lookman na Najeriya a matsayin dan wasa mafi hazaka a nahiyar Afirka a wannan shekarar.

Kuma rahotanni sun bayyana cewa fuskokin abokan tafiyar Achraf Hakimi ne, wadanda sun yi tsammanin shine zai lashe kyautar.

Indai kwallon kafa kake a nahiyar Afirka, Ademola Lookman shine shugabanka a wannan shekarar.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024

Waye gwarzon ɗan ƙwallon kafar Afrika na 2024?

December 16, 2024

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 2024

FAGEN WASANNI – Real Madrid ta kara kaimi wajen zawarcin Alexander-Arnold daga Liverpool

October 9, 2024

Jude Bellingham zaiyi jinyar makwanni

August 23, 2024
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.