Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gobara ta kone shaguna a kasuwar Kurmi dake jihar Kano
Afrika

Gobara ta kone shaguna a kasuwar Kurmi dake jihar Kano

April 18, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2025 04 18 at 16.29.12

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano dake arewacin Najeriya, ƙarƙashin jagorancin Darakta Alhaji Sani Anas, ta ce ta shawo kan wata gobara da ta tashi a kasuwar kurmi tare da kone shaguna shida a layin masu sayar da wayoyin hannu wato yan Jjagwal.

Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Saminu Yusif Abdullahi, ya fitar ga manema labarai ta kara da cewa hukumar kashe gobarar ta karɓi kiran gaggawa daga DPO na ofishin ‘yan sanda na Jakara a ranar Juma’a, 18 ga Afrilu, 2025, da misalin ƙarfe 1:35 na dare, game da gobara da ta tashi a kasuwar Kurmi, unguwar Jakara ‘yan Jagal.

Jami’an hukumar daga babban ofishin suka halarci gurin da gobarar ta faru, inda suka tarar da wasu shaguna shida sun kama da wuta sosai, yayin da wasu shaguna guda biyar suka samu ɗan ɓarna kaɗan, amma ba su ƙone ba.

Sanarwar ta kara da cewa ma’aikatan hukumar kashe gobarar sun nuna ƙwazon wajen shawo kan gobarar cikin lokaci, tare da hana yaduwar wutar zuwa sauran shaguna a kasuwar.

An kuma tseratar da kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

A baya-bayan nan, a ranar Talata 15 ga Afrilu, 2025, an samu irin wannan gobara a wannan kasuwa. Saboda haka, hukumar zata gudanar da bincike don gano musabbabin gobarar da kuma ɗaukar matakin hana faruwar hakan a gaba.

Rahotannin sun tabbatar da cewa ba a samu asarar rai ko raunuka ba a lokacin gobarar.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yawan Al’umma Na Iya Tsananta Matsalar Tsaro a Nijeriya-Bankin Duniya

October 20, 2025

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.