Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gobara ta kone shaguna a kasuwar Kurmi dake jihar Kano
Afrika

Gobara ta kone shaguna a kasuwar Kurmi dake jihar Kano

April 18, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2025 04 18 at 16.29.12

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano dake arewacin Najeriya, ƙarƙashin jagorancin Darakta Alhaji Sani Anas, ta ce ta shawo kan wata gobara da ta tashi a kasuwar kurmi tare da kone shaguna shida a layin masu sayar da wayoyin hannu wato yan Jjagwal.

Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Saminu Yusif Abdullahi, ya fitar ga manema labarai ta kara da cewa hukumar kashe gobarar ta karɓi kiran gaggawa daga DPO na ofishin ‘yan sanda na Jakara a ranar Juma’a, 18 ga Afrilu, 2025, da misalin ƙarfe 1:35 na dare, game da gobara da ta tashi a kasuwar Kurmi, unguwar Jakara ‘yan Jagal.

Jami’an hukumar daga babban ofishin suka halarci gurin da gobarar ta faru, inda suka tarar da wasu shaguna shida sun kama da wuta sosai, yayin da wasu shaguna guda biyar suka samu ɗan ɓarna kaɗan, amma ba su ƙone ba.

Sanarwar ta kara da cewa ma’aikatan hukumar kashe gobarar sun nuna ƙwazon wajen shawo kan gobarar cikin lokaci, tare da hana yaduwar wutar zuwa sauran shaguna a kasuwar.

An kuma tseratar da kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

A baya-bayan nan, a ranar Talata 15 ga Afrilu, 2025, an samu irin wannan gobara a wannan kasuwa. Saboda haka, hukumar zata gudanar da bincike don gano musabbabin gobarar da kuma ɗaukar matakin hana faruwar hakan a gaba.

Rahotannin sun tabbatar da cewa ba a samu asarar rai ko raunuka ba a lokacin gobarar.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Za mu mayar da martani kan harin da aka kai wa jirgin ruwanmu – Koriya ta Kudu

May 11, 2026

Dalilin da ya sa na maida akwatin zaɓena Abuja – Pantami

May 11, 2026

Dangote na shirin gina matatar mai a ƙasar Kenya

May 11, 2026

Samar da Aminci, Shi Ne Farko — Dole a Kawar Da Siyasar Dauka Makamai Daga Fagen Siyasar Kano

May 5, 2026

Pantami ya yi watsi da tsarin maslaha bayan kin daukar shi a matsayin dan takarar gwamnan Gombe

May 3, 2026

Kwankwaso da Obi sun koma jam’iyyar NDC

May 3, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.