Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Akwai alaka mai tsohon tarihi tsakanin Kano da Borno – Gwamna Zulum
Afrika

Akwai alaka mai tsohon tarihi tsakanin Kano da Borno – Gwamna Zulum

September 19, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2024 09 19 at 15.53.04
WhatsApp Image 2024 09 19 at 15.53.04

Gwamnan Jihar Borno Professor Babagana Umara Zulum ya bayyana alakar dake tsakanin Jihar Kano da Maiduguri da cewa tsohuwar alaka ce Mai tsohon tarihi.

Gwamnan Babagana Zulum ya bayyana hakan ne lokacin da yake karbar bakuncin Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero a gidan Gwamnati bisa rakiyar Shehun Borno Alhaji Abubakar ibn Umar Garbai El Kanemi a ziyar jajantawa da Sarkin Kanon ya Kai Jihar Borno.

Gwamna Zulum ya godewa mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero bisa wannan ziyara da ya Kai musu inda yace bazasu taba mantawa da wannan ziyara ba kuma zata Kara karfafa zumuncin dake tsakanin jihohin guda biyu.

Ya bayyana irin asarar rayuka da dukiyoyin da al’umar jihar Borno sukayi da cewa wata babbar asara ce da bazasu iya misalta ta ba Amma yace wata jarrawace daga Allah Yana Mai Kara godiya ga Allah da Gwamnatin Tarayya da al’umar Najeriya bisa tallafi da addu’oin da akayi musu.

A nasa jawabin Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yace yace ya ziyarci garin Maiduguri ne domin jajantawa al’umar jihar Borno da Gwamnatin jihar da kuma Shehun Borno bisa wannan ibtila’i na ambaliyar ruwa data afku.

Alhaji Aminu Ado Bayero yace a madadin al’umar jihar Kano dashi kansa suna Kara jajantawa wadanda suka gamu da wannan ibtila’i inda yayi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.

Mai Martaba Sarkin ya godewa al’umar jihar Borno bisa yadda suka karbeshi, inda yace wannan ba wani abun mamaki bane sakamakon yadda alakar zumunci take a tsakanin al’umar jihar Kano da kuma ta Maidugurin.

Tunda farko da yake jawabinsa lokacin daya karbi bakuncin Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero a fadarsa, Shehun Borno Alhaji Abubakar ibn Umar Garbai El Kanemi ya godewa Alhaji Aminu Ado Bayero bisa wannan ziyara daya kawo kafa da kafa garin na Maiduguri domin jajanta musu bisa ibtila’in ambaliyar ruwa da suka samu.

Shehun Borno Alhaji Abubakar Garbai El Kanemi yayi addu’a da fatan cigaban zumuncinsu da dorewar zaman lafiya da karuwar arziki a jihohin nasu da Kasa baki daya

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yawan Al’umma Na Iya Tsananta Matsalar Tsaro a Nijeriya-Bankin Duniya

October 20, 2025

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.