Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Akwai alaka mai tsohon tarihi tsakanin Kano da Borno – Gwamna Zulum
Afrika

Akwai alaka mai tsohon tarihi tsakanin Kano da Borno – Gwamna Zulum

September 19, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2024 09 19 at 15.53.04
WhatsApp Image 2024 09 19 at 15.53.04

Gwamnan Jihar Borno Professor Babagana Umara Zulum ya bayyana alakar dake tsakanin Jihar Kano da Maiduguri da cewa tsohuwar alaka ce Mai tsohon tarihi.

Gwamnan Babagana Zulum ya bayyana hakan ne lokacin da yake karbar bakuncin Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero a gidan Gwamnati bisa rakiyar Shehun Borno Alhaji Abubakar ibn Umar Garbai El Kanemi a ziyar jajantawa da Sarkin Kanon ya Kai Jihar Borno.

Gwamna Zulum ya godewa mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero bisa wannan ziyara da ya Kai musu inda yace bazasu taba mantawa da wannan ziyara ba kuma zata Kara karfafa zumuncin dake tsakanin jihohin guda biyu.

Ya bayyana irin asarar rayuka da dukiyoyin da al’umar jihar Borno sukayi da cewa wata babbar asara ce da bazasu iya misalta ta ba Amma yace wata jarrawace daga Allah Yana Mai Kara godiya ga Allah da Gwamnatin Tarayya da al’umar Najeriya bisa tallafi da addu’oin da akayi musu.

A nasa jawabin Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yace yace ya ziyarci garin Maiduguri ne domin jajantawa al’umar jihar Borno da Gwamnatin jihar da kuma Shehun Borno bisa wannan ibtila’i na ambaliyar ruwa data afku.

Alhaji Aminu Ado Bayero yace a madadin al’umar jihar Kano dashi kansa suna Kara jajantawa wadanda suka gamu da wannan ibtila’i inda yayi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.

Mai Martaba Sarkin ya godewa al’umar jihar Borno bisa yadda suka karbeshi, inda yace wannan ba wani abun mamaki bane sakamakon yadda alakar zumunci take a tsakanin al’umar jihar Kano da kuma ta Maidugurin.

Tunda farko da yake jawabinsa lokacin daya karbi bakuncin Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero a fadarsa, Shehun Borno Alhaji Abubakar ibn Umar Garbai El Kanemi ya godewa Alhaji Aminu Ado Bayero bisa wannan ziyara daya kawo kafa da kafa garin na Maiduguri domin jajanta musu bisa ibtila’in ambaliyar ruwa da suka samu.

Shehun Borno Alhaji Abubakar Garbai El Kanemi yayi addu’a da fatan cigaban zumuncinsu da dorewar zaman lafiya da karuwar arziki a jihohin nasu da Kasa baki daya

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana aniyarta na fara amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira ta AI wajen gudanar da ayyukan zaɓe a ƙasar

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ta kashe fiye da Naira Biliyan Biyu wajen karbo shidar kammala yan asalin Jihar karatun Dalibai Tamanin da Hudu

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ba zata lamunci Jan kafa ba wajen ajiye mutanen da ake tuhuma da laifi a gidan gyaran Hali

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.