Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Akwai alaka mai tsohon tarihi tsakanin Kano da Borno – Gwamna Zulum
Afrika

Akwai alaka mai tsohon tarihi tsakanin Kano da Borno – Gwamna Zulum

September 19, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2024 09 19 at 15.53.04
WhatsApp Image 2024 09 19 at 15.53.04

Gwamnan Jihar Borno Professor Babagana Umara Zulum ya bayyana alakar dake tsakanin Jihar Kano da Maiduguri da cewa tsohuwar alaka ce Mai tsohon tarihi.

Gwamnan Babagana Zulum ya bayyana hakan ne lokacin da yake karbar bakuncin Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero a gidan Gwamnati bisa rakiyar Shehun Borno Alhaji Abubakar ibn Umar Garbai El Kanemi a ziyar jajantawa da Sarkin Kanon ya Kai Jihar Borno.

Gwamna Zulum ya godewa mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero bisa wannan ziyara da ya Kai musu inda yace bazasu taba mantawa da wannan ziyara ba kuma zata Kara karfafa zumuncin dake tsakanin jihohin guda biyu.

Ya bayyana irin asarar rayuka da dukiyoyin da al’umar jihar Borno sukayi da cewa wata babbar asara ce da bazasu iya misalta ta ba Amma yace wata jarrawace daga Allah Yana Mai Kara godiya ga Allah da Gwamnatin Tarayya da al’umar Najeriya bisa tallafi da addu’oin da akayi musu.

A nasa jawabin Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero yace yace ya ziyarci garin Maiduguri ne domin jajantawa al’umar jihar Borno da Gwamnatin jihar da kuma Shehun Borno bisa wannan ibtila’i na ambaliyar ruwa data afku.

Alhaji Aminu Ado Bayero yace a madadin al’umar jihar Kano dashi kansa suna Kara jajantawa wadanda suka gamu da wannan ibtila’i inda yayi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.

Mai Martaba Sarkin ya godewa al’umar jihar Borno bisa yadda suka karbeshi, inda yace wannan ba wani abun mamaki bane sakamakon yadda alakar zumunci take a tsakanin al’umar jihar Kano da kuma ta Maidugurin.

Tunda farko da yake jawabinsa lokacin daya karbi bakuncin Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero a fadarsa, Shehun Borno Alhaji Abubakar ibn Umar Garbai El Kanemi ya godewa Alhaji Aminu Ado Bayero bisa wannan ziyara daya kawo kafa da kafa garin na Maiduguri domin jajanta musu bisa ibtila’in ambaliyar ruwa da suka samu.

Shehun Borno Alhaji Abubakar Garbai El Kanemi yayi addu’a da fatan cigaban zumuncinsu da dorewar zaman lafiya da karuwar arziki a jihohin nasu da Kasa baki daya

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026

Maki shida ne ya rage tsakanin Arsenal da Man City

April 13, 2026

Mutane sama da 50 sun rasu a kuskuren harin sojin sama a kasuwa

April 13, 2026

INEC ta ɗage aikin sabunta bayanan rajistar masu zaɓe a fadin ƙasa

April 11, 2026

Gwamnan Kano ya naɗa Bilkisu Maimota a matsayin shugabar ma’aikata ta jiha

April 11, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.