Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 
Afrika

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Nig Police force

Rundunar yansanda ta jihar Edo ta kama wasu gungun ɓatagari da su ka haɗa da jami’an ƴansanda biyar da gida ɗaya da aka kora daga aiki, tare da wasu mutum uku, bisa zargin cin zarafi, sace mutane da kuma kwace musu kudade a jihar.

Jami’an da aka kama sun hada da ASP Bonny Paul Onajite, Insifekta Ehubarieme Wisdom, Insifekta Arebame Godspower, Kofur Mordi Philip, Kofur Okon Elvis, da kuma Destiny Emmanuel wanda aka kora daga aikin dan sanda.

Rahoton Daily Trust ya ce sauran wadanda aka kama tare da jami’an sun hada da Goodluck Jaja, mai sana’ar POS, da Samuel Nicholas da Etim Bright, wadanda dukkansu direbobin karamar mota ne.

Mai magana da yawun rundunar, ASP Eno Ikioedem, ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa kungiyar ta kama mutane ne ta hanyar karyar cewa su jami’an tsaro ne, inda suke sace su tare da kwace musu kudade a Benin City.

Ta kara da cewa jami’an da har yanzu suke bakin aiki suna fuskantar matakan ladabtarwa na cikin gida, ciki har da tsarewa kafin daga bisani a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.

A cewarta, gungun ɓatagarin na gudanar da ayyukanta ne a yankin Teboga da ke kusa da Aduwawa, inda suke tilasta wa wadanda suka kama shiga motoci, su zagaya da su a cikin birni kafin a tilasta musu cire kudade ta hanyar POS cikin barazana.

Ta ce kamen ya biyo bayan korafe-korafe da dama daga mazauna yankin kan yadda wasu ke yin kame da kwace kuɗaɗe suna fakewa da sunan ’yan sanda.

Ikioedem ta bayyana lamarin a matsayin babbar barazana ga amincewar jama’a, tana mai cewa ayyukan waɗanda ake zargin sun jawo wa rundunar ’yan sanda ɓacin suna.

Ta kuma gargadi masu sana’ar POS da su guji taimakawa irin wadannan ayyuka na haram, tana mai cewa duk wanda aka samu da hannu a ciki zai fuskanci hukunci.

Sai dai ta bukaci wadanda suka fuskanci wannan abu su fito su bayar da bayanai domin taimakawa bincike, tana mai jaddada kudirin rundunar na tabbatar da gaskiya da adalci.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Rikicin ACF: Lokaci Ya Yi Na Rushe Tsohon Tsari Da Yin Garambawul —Abbas Ibrahim 

May 12, 2026

Za mu mayar da martani kan harin da aka kai wa jirgin ruwanmu – Koriya ta Kudu

May 11, 2026

Dalilin da ya sa na maida akwatin zaɓena Abuja – Pantami

May 11, 2026

Dangote na shirin gina matatar mai a ƙasar Kenya

May 11, 2026

Samar da Aminci, Shi Ne Farko — Dole a Kawar Da Siyasar Dauka Makamai Daga Fagen Siyasar Kano

May 5, 2026

Pantami ya yi watsi da tsarin maslaha bayan kin daukar shi a matsayin dan takarar gwamnan Gombe

May 3, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.