Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Kano: Gwamna Abba ya yi gargaɗin karkatar da tallafin tamowa da jakunkunan ɗalibai
Afrika

Kano: Gwamna Abba ya yi gargaɗin karkatar da tallafin tamowa da jakunkunan ɗalibai

March 30, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
Abba Yusuf

Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta Jihar Kano, ta koka a kan sama da faɗi da ake yi da madarar tamowa ta ƙananan yara masu larurar rashin abinci mai gina jiki tare da handame jakunkunan ɗalibai da ke yankunan ƙananan hukumomi 44 na faɗin jihar.

A bisa haka gwamnatin, ta gindaya doka da oda mai ƙarfi ga dukkan waɗanda suke da alhaki wajen karkatar da irin waɗannan muhimman kayayyakin tagomashin inganta rayuwar al’umar dake kafatanin jihar.

Jami’in Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa Reshen jihar Kano, Malam Balarabe Yusuf Sani, ya nuna damuwa bisa yadda rashin gaskiya da amana suka mamaye jama’a, musamman ganin yadda wasu iyaye ke iya sarayar da tallafi mai alfanu ga rayuwar ‘ya’yansu.

Haka kuma, ya ja hankalin guɓatattun ma’aikatan lafiya su kiyaye aiki cikin tsoron Allah, kamar yadda jami’ar yaɗa labaran ƙaramar hukumar Bichi, Jamila Abdullahi Rijiyar Lemo ta ruwaito.

“Yadda ake rabar da tamowa shi ne, ba kawai zuwa ake da yaro asibiti ana ba shi ba, sai an auna shi an tabbatar yana buƙatarta, sannan a ba shi. Kowace ƙaramar hukuma tana da santar da ake bayarwa; wata santarta ɗaya ne wata ya fi haka, ya dai daganta da yawan yara masu larurar cutar tamowa a kowane yankin.

Kuma duk sadda yakamata a dawo karɓar wa yaro, to a zo da shi ne a sake auna shi, idan nauyinsa ya ƙaru tabbas ana yi masa amfani da tamowar, idan kuma bai ƙaru ba, to alamu ne ana karkatar masa da ita kasuwa ko ana shanye masa!” Jami’in Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa Reshen jihar Kano, Malam Balarabe Yusuf Sani.

Daraktar Ayyuka na Musamman a Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin-gida ta jihar Kano, Hajiya Halima Ahmad Ishaq, ta ja hankalin al’uma dangane da alkinta dukiya da kadarorin gwamnati domin amfanar kai-da-kai, sannan ta yi kira ga iyaye mata su kula da haƙƙoƙin ‘ya’yansu ta fuskar ilimi da tarbiya, musaman kiwon lafiyar yara masu larurar tamowa.

“Lallai ne a ja hankalin mutane, musamman mata, don Allah don Annabi su daina sayar da tamowar da ake bai wa ‘ya’yansu tallafi, ko shanye musu, ko su ƙyale iyaye maza su amshe, ko bai wa masu reno, ko kuma sayar wa mata masu ciki, wannan duk bai kamata ba!” Daraktar Ayyuka na Musamman a Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin-gida ta jihar Kano Hajiya Halima Ahmad Ishaq.

A jawabin Shugaban Sashen Kula da Lafiya na Bichi, Malam Kabiru Abubakar Gwarzo, wanda Malam Isa Shitu ya wakilce shi, ya ba da tabbacin za su sa ido ga ma’aikatan lafiyar yankin wajen kawar da matsalar.

Kazalka, Sakataren Hakimin Bichi, Galadiman Kano Alhaji Mannir Sanusi, Malam Idris Shitu Malikawa da ya yi magana a madadinsa, ya ce, za su yi bakin ƙoƙarinsu wajen fadakar da al’umar Ƙaramar Hukumar Bichi domin magance irin waɗannan matsaloli a yankin baki ɗaya.

Zaman ya haɗa da; wakilin Asusun Tallafa wa ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF), Malam Yunusa Ahmad, wakilin Hakimin Bichi, jami’in Hukumar Wayar da Kan “Yan Kasa Reshen jihar Kano da wakilin sashen lafiya na yankin.

 

Blueprint

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.