Fadar Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ta sanar da rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, cewa ta fara shirye-shiryen gudanar da bukukuwan Hawan Salla idan an kammala azumin watan Ramadan.
Wannan na cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 7 ga watan Maris, 2026, wadda aka aike wa Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori.
Jami’an NDLEA Sun Kama Mutane 56 A Wuraren Hada-hadar Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Fadar ta ce za a gudanar da bukukuwan hawan sallar daga fadar sarkin da ke unguwar Nassarawa a Kano.

