Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Tinubu ya sake naɗa Abubakar Audi a Kwamanda Janar Na NSCDC
Afrika

Tinubu ya sake naɗa Abubakar Audi a Kwamanda Janar Na NSCDC

February 28, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
NSCDC CG Ahmed Abubakar Audi

Shugaba Bola Tinubu ya sake naɗa Dakta Ahmed Abubakar Audi a matsayin Kwamanda-Janar na Hukumar Tsaron al’umma ta Cibil Defense (NSCDC) na wani sabon wa’adin shekaru biyar.

Sabon naɗin ya fara aiki ne q ranar Juma’a, 27 ga Fabrairu, 2026 .

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

An fara naɗa Dakta Audi a wannan matsayi ne a shekarar 2021 ta hannun tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari. Wa’adinsa na farko na shekaru biyar ya ƙare ne a ranar Juma’ar da ta gabata yayin da yake halartar bikin Ranar Kariya ta Duniya ta 2026 a hedikwatar NSCDC ta ƙasa da ke Abuja.

Litinin mai zuwa ake sa ran Audi zai koma bakin aikinsa ranar tare da sabon ƙuduri da sabon wa’adi.

Shugaba Tinubu ya umarci Audi da ya sake fasalta da inganta hukumar domin ta taka muhimmiyar rawa a harkokin tsaron ƙasa, musamman a lokacin da rundunar ’yan sanda ke mai da hankali kan babban aikinta na kare ’yan ƙasa daga ’yan fashi da makami, masu garkuwa da mutane da ’yan ta’adda.

An haifi Dakta Audi a ranar 30 ga Satumba, 1967 a garin Laminga, Ƙaramar Hukumar Nasarawa, Jihar Nasarawa. Bayan ya kammala karatunsa na farko a jihar, ya halarci Kwalejin Horar da Malamai ta Jengre a Jihar Plateau, inda ya samu takardar shaidar Teachers’ Grade II a shekarar 1987.

Daga nan ya wuce Kwalejin Ilimi ta Akwanga, inda ya samu takardar shaidar NCE a shekarar 1992. Saboda ƙwazon neman ilimi, ya shiga Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ya kammala digirinsa na farko a fannin Ilimin Jiki da Lafiya (Physical and Health Education) a shekarar 1995.

A shekarar 2001 ya samu digiri na biyu (Masters) a fannin Gudanar da Harkokin Mulki (Public Administration) daga Jami’ar Calabar. A shekarar 2014 ya samu digirin digirgir (PhD) a fannin Public Administration daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi, sannan a shekarar 2019 ya sake samun digiri na biyu a fannin Law Enforcement and Criminal Justice (MLCJ) daga Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Dakta Audi ya shiga NSCDC a watan Nuwamba 1996 a matsayin mai aikin sa kai, sannan aka tura shi a matsayin Jami’in Rukuni (Divisional Officer) a ƙaramar hukumar Obi, Jihar Nasarawa, bayan ya kammala horon jami’ai a shekarar 1997.

Ya yi aiki a sassan jihohi daban-daban, kuma a shekarar 2007 aka ɗaga shi zuwa mukamin Commandant na Hukumar, daga bisani aka tura shi ofishin Kwamanda-Janar a Hedikwatar Ƙasa da ke Abuja.

NSCDC
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamnan Kano ya sauke shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Abdullahi Musa daga mukaminsa

March 11, 2026

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

By WafsymMarch 11, 2026

Sabbin matakan da Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dauka na fara shirin tsige Mataimakin Gwamna,…

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.