Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎
Bincike Na Musamman

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260227 WA0012

Daga Salisu Ibrahim Fagge tare da haɗin gwiwar Abbas Ibrahim, Mohammed Kabir Yau, Abdullahi Yusuf, Mustapha Muhammad da Kabiru Fulatan

 

‎Kasuwancin dabbobi a Kano na kara bunƙasa cikin sauri, yayin da buƙatar nama, madara da fata ke ƙaruwa a sassan Najeriya.

‎Amma duk da wannan ci gaba, wani bincike na musamman ya nuna cewa ana fuskantar babbar barazana ta ɓoye sakamakon yawaitar amfani da wani sinadarin magani da ake yiwa lak’abi da (kira) “Sha Ka Fashe.”

‎Jam’iyyun Adawa Sun Yi Fatali Da Sabuwar Dokar Zabe Ta 2026 Wacce Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ita

‎Binciken ya gano cewa wasu ’yan kasuwar dabbobi na amfani da wannan sinadari domin sa shanu da tumaki su K’ara kiba cikin gaggawa, don su jawo hankalin masu saye a kasuwa.

‎Rahotanni sun nuna cewa “Sha Ka Fashe” da aka fi dangantawa da ƙara kiba a jikin ɗan adam, yanzu ana ba dabbobi domin su yi girma cikin kankanin lokaci.

‎Masana sun yi gargadin cewa hakan na iya cutar da lafiyar jama’a, domin samuwar magunguna a nama na iya haifar da matsaloli masu tsanani, ciki har da cututtuka.

‎Wasu masu sayen dabbobi sun koka da asarar dukiya bayan sayensu. Dabbobin a bayyane masu ƙoshin lafiya ne, amma daga baya sai su kamu da rashin lafiya ko ma ta kai ga mutuwarsu cikin k’ank’anin lokaci.

‎Malam Muhammad Balarabe ya ce ya sayi saniya cikakkiya mai ƙiba a zahiri ga alamun ƙarfi da lafiya a ido, amma cikin kwanaki kaɗan ta kamu da gudawa mai tsanani kuma ta mutu. Ya ce irin wannan lamari na buƙatar Gwamnati ta dauki matakan gaggawa domin maganta lamarin.

‎Jami’an Hukumar Kula da abinci da Magunguna ta Kasa NAFDAC sun ce sun kama magungunan jabu, kuma sun rufe masana’antun da ke samar da ire iren wadannan magungunan dabbobi ba tare da rajista ba, tare da gurfanar da masu laifi a kotu.

Ana ta bangaren ma’aikatar kula da kiwon dabbobi ta jihar Kano, ta bullo da tsari domin yin rajistar wuraren kiwo da bibiyar masu sayar da magungunan dabbobi domin a inganta lafiyar al’umma.

‎Masana da masu ruwa da tsaki sun ce idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba, matsalar za ta iya zama barazana ga lafiyar jama’a, tattalin arziki da Kuma samar da  abinci.

‎Sun buƙaci a sami tsauraran dokoki kan amfani da magungunan dabbobi, kuma a baiwa ‎wayar da kan jama’a a kan haɗarin nama maras inganci muhimmanci, sannan a tallafa wa manoma masu bin ƙa’ida, da kafa cikakkiyar mayanka da za ta gudanar da ayyukanta bisa tsarin halal, a inda ƙwararru ma’aikata za su rinka kula da mayankar.

‎Yayin da kasuwancin dabbobi ke ci gaba da bunƙasa a Kano, jama’a na fatan a ɗauki mataki cikin gaggawa domin hana wannan matsala ta zama barazana ga rayuwar al’umma..

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Majalisar Dokokin Kano ta fara yunƙurin tsige mataimakin Gwamna

March 6, 2026

BINCIKE: An samu karin kashi 543% a yaduwar cutar dajin dake kama nono a Najeriya

March 4, 2026

Shugaba Tinubu ya taya murna ga waɗanda suka lashe zaɓukan Abuja, Kano da Rivers

February 23, 2026

Rundunar ‘yan sandan Kano ta sanya dokar takaita zirga-zirga a kananan hukumomin birnin kano da Ungogo

February 21, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

By WafsymMarch 9, 2026

‎Rundunar Kano Neighbourhood Watch Security Corps, wadda gwamnatin Jihar Kano ta kafa domin tallafawa hukumomin…

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026

‎“Ya Kamata ‘Yan Jaridu Su Riƙa Nuna Tausayi, Hikima Da Mutunta Jinƙan Ɗan Adam wajen ɗauko labarai ‎ ‎ ‎—Comrade Abbas Ibrahim

January 21, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.