Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Jam’iyyun Adawa Sun Yi Fatali Da Sabuwar Dokar Zabe Ta 2026 Wacce Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ita
Afrika

Jam’iyyun Adawa Sun Yi Fatali Da Sabuwar Dokar Zabe Ta 2026 Wacce Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ita

February 27, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260227 WA0001

Wasu jam’iyyun siyasa na adawa a Nijeriya sun yi watsi da Dokar Zabe ta 2026 da Majalisar Dokoki ta Kasa ta amince da ita kuma Shugaba Bola Tinubu ya rattaba wa hannu, inda suka bukaci a fara sabon gyara cikin gaggawa kan abin da suka kira “tanade-tanade masu tauye dimokuradiyya” a cikin dokar.

A wani taron manema labarai mai taken “Kiran Gaggawa Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya” da aka gudanar a Abuja a ranar Alhamis, shugabannin adawar sun ce dokar a yadda take yanzu na iya raunana gaskiya da sahihancin zabe tare da rage amincewar jama’a da tsarin kada kuri’a.

Yayin da yake karanta sanarwar taron, Shugaban Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Ahmed Ajuji, ya ce: “Muna bukatar Majalisar Dokoki ta Kasa ta fara sabon gyara ga Dokar Zabe ta 2026 nan take, domin cire dukkan tanade-tanade marasa kyau tare da tabbatar da cewa dokar ta yi daidai da muradi da burin ‘yan Nijeriya na samun sahihin zabe mai gaskiya, adalci da rikon amana a kasarmu. Kasa da haka ba zai wadatar ba.”

Daga cikin manyan jiga-jigan da suka halarci taron akwai tsohon Shugaban Majalisar Dattawa David Mark, tsohon gwamnan Jihar Osun Rauf Aregbesola, tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, tsohon gwamnan Jihar Rivers Rotimi Amaechi, da kuma tsohon gwamnan Jihar Anambra Peter Obi, duk daga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Manyan Labarai INEC ta sauya jadawalin Zaɓen 2027

Haka kuma, Shugaban NNPP na kasa Ahmed Ajuji da wasu fitattun ‘yan jam’iyyar ciki har da Buba Galadima sun halarta.

Tanade-tanade da Suka Jawo Ce-ce-ku-ce

Daya daga cikin muhimman batutuwan da suka fi daukar hankalin adawar shi ne gyaran Sashe na 60(3), wanda ya bai wa jami’an zabe damar komawa amfani da aika sakamakon zabe ta takarda idan aka samu matsalar sadarwa.

A cewar hadakar jam’iyyun, wannan tanadi na iya raunana wajabcin watsa sakamakon zabe ta na’ura, kuma zai iya samar da gibin da za a iya amfani da shi wajen magudi.

Sun ce kayayyakin fasahar zabe a Nijeriya sun isa su tallafa watsa sakamako ta na’ura a fadin kasa baki daya, suna mai nuni da bayanan da jami’an Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) suka tabɓ bayarwa a baya.

Jam’iyyun sun kuma yi watsi da gyaran Sashe na 84, wanda ya takaita hanyoyin zaben fidda gwani ga jam’iyyun siyasa zuwa zaben kai tsaye (direct primaries) ko kuma tsarin maslaha (consensus).

A cewarsu, wannan sauyi katsalandan ne cikin harkokin cikin gida na jam’iyyun siyasa, suna jaddada cewa zaben fidda gwani na wakilai (indirect primaries) hanya ce halastacciya a tsarin dimokuradiyya.

Sun kuma yi nuni da abin da suka kira kura-kurai a zabukan kananan hukumomi na Babban Birnin Tarayya (FCT) da aka gudanar kwanan nan, inda suka bayyana zaben a matsayin “cikakken magudi.” A cewarsu, hakan ya kara raunana amincewarsu da ikon tsarin zabe na samar da sahihin zabe a shekarar 2027.

Jam’iyyun sun ce matukar ba a sake duba Dokar Zabe ta 2026 baki daya ba, akwai barazanar ci gaba da raguwa amincewar jama’a da tsarin dimokuradiyyar Nijeriya.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026

Majalisar Dokokin Kano ta fara yunƙurin tsige mataimakin Gwamna

March 6, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

By WafsymMarch 9, 2026

‎Rundunar Kano Neighbourhood Watch Security Corps, wadda gwamnatin Jihar Kano ta kafa domin tallafawa hukumomin…

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026

‎“Ya Kamata ‘Yan Jaridu Su Riƙa Nuna Tausayi, Hikima Da Mutunta Jinƙan Ɗan Adam wajen ɗauko labarai ‎ ‎ ‎—Comrade Abbas Ibrahim

January 21, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.