Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya
Afrika

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
FB IMG 1773006543246

Daga wannan Lahadi farashin man fetur a birnin Legas na Najeriya ya yi tashin gwauron zabi, inda yanzu ya kai tsakanin ₦1,040 zuwa ₦1,080 a kowace lita a gidajen mai daban-daban.

Wannan ƙarin ya biyo bayan hauhawar farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya, sakamakon faɗaɗa yaƙi tsakanin kasashen Amurka, Isra’ila, da kuma Iran wanda ke barazana ga harkar man fetur.

Tashin hankali a yankin Gabas Ta Tsakiya, wanda ya haɗa da hare-hare kan jagororin Iran da cibiyoyin man fetur, ya sanya farashin ɗanyen mai na Brent ya kusanci dala $90 zuwa $100 a kowace ganga.

Wannan lamari ya jefa kasuwannin duniya cikin ɗar-ɗar, wanda ke shafar kasashe masu shigo da tataccen mai kamar Najeriya kai-tsaye.

A nan gida, matatun mai sun fara daidaita farashinsu don dacewa da halin da ake ciki, inda matatar man Dangote ta kara farashi daga ₦874 zuwa ₦995 a cikin kwanaki huɗu kacal.

Kamfanin ya bayyana cewa tsadar danyen mai da ake sayowa don tacewa ita ce babban dalilin da ya tilasta wannan karin farashin.

Gidajen man na kamfanin NNPC Retail da ke sassan Legas su ma sun sauya farashinsu zuwa kusan ₦1,040 a kowace lita, daga tsohon farashin da yake kusan ₦993.

Sauran gidajen mai masu zaman kansu irinsu Techno Oil, Mobil, da MRS su ma suna sayar da man a kan farashi daban-daban da ya kama daga ₦1,050 har zuwa kusan ₦1,100 a wasu wuraren.

Masana tattalin arziki sun yi gargadin cewa idan har rikicin Iran ya kai ga toshe mashigin ruwa na Hormuz, farashin ɗanyen mai na iya haura dala $120 zuwa $130 akan kowace ganga.

Idan hakan ta faru, akwai yiwuwar farashin fetur a Najeriya ya kai ₦1,200 ko fiye da haka, wanda zai kara tsananta halin rayuwa ga talaka.

Wannan hauhawar farashin man tuni ya fara shafar farashin abinci da sufuri a fadin kasar, yayin da direbobin motocin haya ke korafin tsadar man. Jama’a na ci gaba da sanya ido kan yadda diflomasiyyar duniya za ta karkata don ganin ko za a samu saukin wannan rikici da ya addabi tattalin arzikin duniya.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

NWUK Expels 34 Students Over Examination Malpractice

June 30, 2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.