Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Dakarun Soji Sun Daƙile Harin Lakurawa Kan Wata Kasuwa a Kebbi
Afrika

Dakarun Soji Sun Daƙile Harin Lakurawa Kan Wata Kasuwa a Kebbi

February 24, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
An yi wata musayar wuta tsakanin sojojin Najeriya da tawagar dan taadda Bello Turji 768x388

Dakarun Sojin Najeriya da ke cikin runduna ta musamman mai yaƙi da ayyukan ta’addanci a yankin arewa maso yammacin ƙasar wato Fansar Yamma sun sanar da nasarar kashe tarin ƴan ta’addan Lakurawa a jihar Kebbi a dai dai lokacin da ƴan ta’addan suka nufaci kai wani hari a jihar Kebbi.

Masanin tsaron yankin tafkin Chadi Zagazola Makama da ke sanar da wannan nasara ta dakarun Sojin Najeriyar a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, ya ce tun da farko ƴan ta’addan suka ɗauki azamar kai hari wata kasuwar ƙauye ce a safiyar jiya Lahadi da ke garin Daɗin kowa a jihar Kebbi amma kuma Sojin Najeriyar suka yi musu tara-tara tare da kashe da dama daga cikinsu.

Ana ci gaba da matsa wa DSS lamba kan ta saki Walida

Makama ya bayyana cewa da farko ƴan ta’addan Lakurawan sun toshe hanyoyi da nufin zagaye yankin da suke son kaiwa harin, gabanin juyewar lamarin zuwa kansu.

Majiyoyi sun ce cikin gaggawa dakarun Sojin Najeriyar suka kai ɗauki bayan samun bayanai daga al’ummar yankin game da yunƙurin harin na Lakurawa, lamarin da ya juye zuwa ga musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu

A cewar bayanai daga majiyoyin yankin ruwan wutar da sojin Najeriyar suka yiwa ƴan ta’addan ba ƙaƙƙautawa ne ya tialsta musu janyewa cikin hanzari kodayake sojojin sun kashe da dama daga cikinsu yayinda wasu suka tsere da raunuka a jikinsu.

 

RFI

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026

Shekaru 12 bayan sace ƴan matan Chibok

April 15, 2026

Tsagin ADC ƙarƙashin David Mark ya kori Nafiu Bala da wasu bisa zargin yi wa jam’iyya zagon-ƙasa

April 15, 2026

Hukumomin yaƙi da cin hanci ba su taɓa gayyata ta ba — Pantami

April 14, 2026

An kama jami’an ƴansanda 6 tare da wasu mutane 3 bisa zargin ƙwace da satar mutane a Edo 

April 14, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

By WafsymApril 2, 2026

A Jihar Kano, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda wasu masu anfani da…

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.