Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Ana ci gaba da matsa wa DSS lamba kan ta saki Walida
Afrika

Ana ci gaba da matsa wa DSS lamba kan ta saki Walida

February 24, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
f69eabf6 97ec 4014 97cc 2f385974e3a2.jpg

Wani lauya mai rajin kare haƙƙin bil’adama a Najeriya, Barista Hamza Nuhu Dantani ya rubuta wata wasiƙa zuwa ga Hukumar tsaron farin kaya DSS ta ƙasar, inda yake nuna damuwa dangane da yadda ya ce hukumar ta ɗauki batun zargin sacewa, da kuma yin lalata da wata mace, Walida Abdulhadi, da ake zargin ɗaya daga cikin jami’anta Ifeanyi Onyewuenyi da yi.

A cikin wasiƙar, lauyan ya saka ayar tambayar kan dalilan ƙin miƙa yarinyar ga iyayenta da kuma abin da ya kira ƙoƙarin kare jami’in da hukumar ke yi.

Ƴan Bindiga sun sa harajin miliyan 100 ga malaman da ke son yin wa’azi a Kebbi

Batun matashiyar na ci gaba da ɗaukar hankali a Najeriya tun bayan da wasu gungun lauyoyi suka shigar da ƙara suna zargin wani jam’in hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (DSS) da laifin “sacewa da yin lalata da kuma sauya wa wata yarinya mai suna Walida Abdulhadi addini.”

 

Rahotanni sun bayyana cewa jami’in na hukumar DSS ne ya tuntuɓi iyayen yarinyar, inda ya shaida musu cewa yana riƙe da ita, kuma har ta haifa masa ɗa, a wata unguwa da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

 

A cikin koken da Barista Nuhu ya rubuta, ya ce “An ɗauke yarinyar ne a lokacin da take aji biyu a babbar sakandare, kuma mahaifinta ya sha nanata cewa ƙaramar yarinya ce a lokacin da ta ɓace.”

 

Lauyan ya buƙaci a miƙa ta zuwa ga iyayenta, inda ya ƙara da cewa babu dokar da ta ba DSS damar ci gaba da riƙe matashiyar. “Don haka ina kira da a saki Walida ba tare da ɓata lokaci ba, sannan wasu daban su gudanar da bincken ba DSS ba.”

Haka kuma wasu ƙungiyoyin rajin kare haƙƙin ɗan’adam sun kai nasu koken, inda suka buƙaci DSS ta gaggauta sakin Walida, domin a cewarsu tana ƴar shekara 16 ne ya tafi da ita.

Ƙungiyoyin, waɗanda suka rubuta koken a ƙarƙashin Gamji Lawchain a madadin mahaifin yarinyar, sun yi zargin cewa jam’in ya sace ta, sannan ya yi lalata da ita, tare da tilasta mata komawa addinin Kirista.

Daga cikin ƙungiyoyin akwai International Human Rights Commission Relief Fund Trust (IHRC-RFT) da Women Voices and Accountability da Muslim Rights Concern (MURIC) da sauransu.

 

BBC

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamnan Kano ya sauke shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Abdullahi Musa daga mukaminsa

March 11, 2026

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

By WafsymMarch 11, 2026

Sabbin matakan da Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dauka na fara shirin tsige Mataimakin Gwamna,…

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.