Wani lauya mai rajin kare haƙƙin bil’adama a Najeriya, Barista Hamza Nuhu Dantani ya rubuta wata wasiƙa zuwa ga Hukumar tsaron farin kaya DSS ta ƙasar, inda yake nuna damuwa dangane da yadda ya ce hukumar ta ɗauki batun zargin sacewa, da kuma yin lalata da wata mace, Walida Abdulhadi, da ake zargin ɗaya daga cikin jami’anta Ifeanyi Onyewuenyi da yi.
A cikin wasiƙar, lauyan ya saka ayar tambayar kan dalilan ƙin miƙa yarinyar ga iyayenta da kuma abin da ya kira ƙoƙarin kare jami’in da hukumar ke yi.
Ƴan Bindiga sun sa harajin miliyan 100 ga malaman da ke son yin wa’azi a Kebbi
Batun matashiyar na ci gaba da ɗaukar hankali a Najeriya tun bayan da wasu gungun lauyoyi suka shigar da ƙara suna zargin wani jam’in hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (DSS) da laifin “sacewa da yin lalata da kuma sauya wa wata yarinya mai suna Walida Abdulhadi addini.”
Rahotanni sun bayyana cewa jami’in na hukumar DSS ne ya tuntuɓi iyayen yarinyar, inda ya shaida musu cewa yana riƙe da ita, kuma har ta haifa masa ɗa, a wata unguwa da ke Abuja, babban birnin Najeriya.
A cikin koken da Barista Nuhu ya rubuta, ya ce “An ɗauke yarinyar ne a lokacin da take aji biyu a babbar sakandare, kuma mahaifinta ya sha nanata cewa ƙaramar yarinya ce a lokacin da ta ɓace.”
Lauyan ya buƙaci a miƙa ta zuwa ga iyayenta, inda ya ƙara da cewa babu dokar da ta ba DSS damar ci gaba da riƙe matashiyar. “Don haka ina kira da a saki Walida ba tare da ɓata lokaci ba, sannan wasu daban su gudanar da bincken ba DSS ba.”
Haka kuma wasu ƙungiyoyin rajin kare haƙƙin ɗan’adam sun kai nasu koken, inda suka buƙaci DSS ta gaggauta sakin Walida, domin a cewarsu tana ƴar shekara 16 ne ya tafi da ita.
Ƙungiyoyin, waɗanda suka rubuta koken a ƙarƙashin Gamji Lawchain a madadin mahaifin yarinyar, sun yi zargin cewa jam’in ya sace ta, sannan ya yi lalata da ita, tare da tilasta mata komawa addinin Kirista.
Daga cikin ƙungiyoyin akwai International Human Rights Commission Relief Fund Trust (IHRC-RFT) da Women Voices and Accountability da Muslim Rights Concern (MURIC) da sauransu.

