Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Kotu Ta Ci Tarar Ƴansanda Naira Miliyan 30 Kan Ayyana Neman Sowore Ruwa A Jallo
Afrika

Kotu Ta Ci Tarar Ƴansanda Naira Miliyan 30 Kan Ayyana Neman Sowore Ruwa A Jallo

February 22, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
imaigpges 1 1 750x375

Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta yanke hukunci cewa Rundunar ‘Yansandan Nijeriya, ta aikata kuskure da ya saɓa ƙa’ida na ayyana ɗan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan Adam kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore, a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo a shekarar 2025.

Yayin yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai shari’a Musa Kakaaki, ya bayyana cewa matakin da ’yansanda suka ɗauka ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulki tare da nuna amfani da iko da bai dace ba, inda ya jaddada cewa babu wanda ya zama mai laifi saboda amfani da ’yancin faɗar albarkacin bakinsa ko gudanar da zanga-zangar lumana ko kuma neman gwamnati ta ɗauki alhakin wani laifinta.

Abin da ya sa na shiga siyasa tsundum – Sheikh Pantami

Alƙalin ya ƙara da cewa ba za a ayyana mutum a matsayin wanda ake nema ba sai an samu sahihin sammacin kotu tare da ba shi cikakken sanarwa, kuma akwai hujjoji masu ƙarfi da ke nuna cewa yana guje wa shari’a da gangan.

Daga bisani kotun ta yanke hukuncin biyan diyyar Naira miliyan 30 a kan Rundunar ƴansanda da Sufeto Janar na ’Yansanda, Kayode Egbetokun, da Kwamishinan ’Yansandan Jihar Legas, Moshood Jimoh.

Idan ba a manta ba, a ranar 3 ga Nuwamban 2025, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Legas, Moshood Jimoh, ya ayyana Omoyele Sowore a bainar jama’a a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo, inda ya zarge shi da yunƙurin shirya zanga-zangar a kan gadar jihar ta “Third Mainland Bridge“ sakamakon rushe wasu gine-gine a unguwar Oworonshoki.

 

 

LEADSHIP

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamna Abba Ya Kaddamar da Kwamitin Yaƙi da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Ya Sanya Hannu Kan Dokar Daba A Kano

July 22, 2026

“Rikicin Shaidar Zama Ɗan Ƙasa a Jos North Ya Ɗauki Sabon Salo, Sarakunan Gargajiya Sun Nemi Shiga Cikin Shari’a.”

July 11, 2026

Sarkin Gaya: Mallakar Katin Zaɓe Shi Ne Ginshiƙin Zaɓen Shugabanni Nagari

July 3, 2026

Sahihin ‎Labari Ke Tabbatar Da Amincewar Jama’a, Ba Gaggawar Wallafa Ba- Shugaban NUJ

July 1, 2026

NWUK Expels 34 Students Over Examination Malpractice

June 30, 2026

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Gwamnatin Kano Ta Yi Alƙawarin Ƙara Wa NDLEA Motoci Don Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ‎

June 29, 20267

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.