Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta yanke hukunci cewa Rundunar ‘Yansandan Nijeriya, ta aikata kuskure da ya saɓa ƙa’ida na ayyana ɗan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan Adam kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore, a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo a shekarar 2025.
Yayin yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai shari’a Musa Kakaaki, ya bayyana cewa matakin da ’yansanda suka ɗauka ya saɓa wa tanade-tanaden kundin tsarin mulki tare da nuna amfani da iko da bai dace ba, inda ya jaddada cewa babu wanda ya zama mai laifi saboda amfani da ’yancin faɗar albarkacin bakinsa ko gudanar da zanga-zangar lumana ko kuma neman gwamnati ta ɗauki alhakin wani laifinta.
Abin da ya sa na shiga siyasa tsundum – Sheikh Pantami
Alƙalin ya ƙara da cewa ba za a ayyana mutum a matsayin wanda ake nema ba sai an samu sahihin sammacin kotu tare da ba shi cikakken sanarwa, kuma akwai hujjoji masu ƙarfi da ke nuna cewa yana guje wa shari’a da gangan.
Daga bisani kotun ta yanke hukuncin biyan diyyar Naira miliyan 30 a kan Rundunar ƴansanda da Sufeto Janar na ’Yansanda, Kayode Egbetokun, da Kwamishinan ’Yansandan Jihar Legas, Moshood Jimoh.
Idan ba a manta ba, a ranar 3 ga Nuwamban 2025, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Legas, Moshood Jimoh, ya ayyana Omoyele Sowore a bainar jama’a a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo, inda ya zarge shi da yunƙurin shirya zanga-zangar a kan gadar jihar ta “Third Mainland Bridge“ sakamakon rushe wasu gine-gine a unguwar Oworonshoki.
LEADSHIP

