Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nuna matuƙar alhini kan rasuwar aƙalla mutane 30 da suka mutu sakamakon mummunan hatsarin mota da ya faru a Kwanar Barde dake ƙaramar hukumar Gezawa.
Gwamnan ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu a ranar Lahadi.
Gwamnatin Kano Ta Nemi Haɗin Kan ’Yan Kasuwa Don Rage Tsadar Kayayyaki A Ramadan
Ya bayyana hatsarin a matsayin abin tausayi da babban rashi ba ga iyalan mamatan kaɗai ba, har ma ga daukacin al’ummar Jihar Kano.
Rahotanni sun nuna cewa hatsarin ya faru ne sakamakon wata tirela da ke kan hanyar zuwa Gujungu, wadda ake zargin direbanta da tuƙi cikin ganganci ta yi taho mu gama da wata motar fasinjoji.
Mutane fiye da 30 ne aka tabbatar sun rasa rayukansu, yayin da wasu da dama suka samu munanan raunuka, kuma suna karɓar magani a asibitoci daban-daban a faɗin jihar.
Gwamna Yusuf ya yi addu’ar Allah ya jikan waɗanda suka rasu, tare da roƙon Allah ya bawa iyalansu haƙurin jure wannan babban rashi. Haka kuma ya yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi cikin gaggawa.
Ya umarci Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano da ta tabbatar duk waɗanda hatsarin ya shafa ana ba su cikakken magani kyauta ba tare da wani jinkiri ba.

