Babban Kotun Jihar Bauchi mai lamba hudu, ta yanke wa wani mutum mai suna Mamuda Zakariyau hukuncin kisa ta hanyar rataya, bisa laifin kashe wani mai babur da wuƙa a lokacin da ya yi yunƙurin satar babur ɗin.
Da yake yanke hukuncin, alkalin kotun, Mai Shari’a Aliyu Baba Usman, ya ce: “Saboda kotu ta same ka da aikata laifin kisan kai, wanda hukuncinsa kisa ne, an yanke maka hukuncin kisa ta hanyar rataya.”
Kotu ta bayar da belin mutanen da suka bayar da shedar kanzon Kurege kan kisan Dorayi
Lauyoyin Ma’aikatar Shari’a sun gabatar da tuhuma guda biyu a kan Mamuda, inda suka ce a ranar 16 ga watan Oktoba, 2026, Mamuda ya haɗa baki da wani Sadiq, wanda aka fi sani da Gwaska (wanda ake nema a yanzu), suka hau babur ɗin Basiru Mohammed.

