Tsohon Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ), reshen jihar Kano, Comrade Abbas Ibrahim, ya jaddada muhimmancin gudanar da aikin jarida cikin tausayawa da hikima, musamman wajen ɗauko labarai da suka shafi masifu, raɗaɗi ko wahalhalun rayuwar mutane.
A cewarsa, aikin jarida ba wai tattara bayanai kawai ba ne, har da la’akari da halin da mutumin da abin ya shafa yake ciki.
Tsadar Data Ta Jefa Ɗaliban Karatu Daga Nesa Cikin Ƙunci A Najeriya
“Ya kamata a dubi yanayin mutum kafin a fara yi masa tambayoyi, musamman idan yana cikin damuwa ko rashin lafiya,” in ji Abbas Ibrahim.
Ya lura cewa wasu ’yan jarida na yin tambayoyi a wuraren da ba su dace ba, ko ɗaukar hotuna da bidiyo ba tare da neman izini ba, abin da yake sabawa ƙa’idojin aikin jarida da dokokin sana’a.
“Idan ba mu mutunta jinƙan ɗan Adam ba, muna rage amincewar al’umma a kan aikin jarida,” in ji shi.
Comrade Abbas Ibrahim ya ƙara da cewa mutunta haƙƙin mutane da bin ƙa’ida shi ne ginshiƙin martabar aikin jarida, tare da tabbatar da cewa labarai ba sa ƙara jefa mutane cikin raɗaɗi.

