Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Hukumar Alhazan Nijeriya ta fitar da farashin kujerar Aikin Hajjin 2026
Afrika

Hukumar Alhazan Nijeriya ta fitar da farashin kujerar Aikin Hajjin 2026

September 28, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
NAHCON

Hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta sanar da kuɗin Aikin Hajji na shekara mai zuwa ta 2026 da aka ƙayyade kan naira miliyan 8.1, miliyan 8.2 da miliyan 8.5.

Shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ne ya sanar da hakan bayan rattaba hannu kan wasu yarjejeniyoyi da kamfanonin da ke tafiyar da hidimomin alhazai a ƙasar Saudiyya.

Wata sanarwa daga sashen yaɗa labarai na hukumar ya fitar ta ce: “Bayan tuntubar duka masu ruwa da tsaki, ciki har da shugabannin jihohi da samun amincewar Gwamnatin Tarayya da Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya sanar da kuɗin Hajjin 2026 kamar haka:
– Yankin Maiduguri–Yola (Yobe, Borno, Adamawa da Taraba) za su biya N8,118,333.67.
– Sauran jihohin Arewa za su biya N8,244,813.67.
– Jihohin Kudancin ƙasar za su biya N8,561,013.67.

Idan aka kwatanta da abin da aka biya bara, a bana kowane maniyyaci zai samu ragin aƙalla naira 200,000.”
Wakilan Hukumar NAHCON da a halin yanzu suke a Saudiyya sun gana tare da sanya hannu kan yarjejeniya da kamfanin da zai yi hidimar alhazai a shekarar 2026 wato kamfanin Mashareeq Al-Zahabiyya da kuma kamfanin sufuri na Daleel Al-Ma’aleem.

Farfesa Usman ya ja hankalin duk masu niyyar zuwa Aikin Hajji su kammala biyan kuɗin su kafin 31 ga Disamba 2025.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano

January 12, 2026

Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Kuɗin 2026 Na Naira Tiriliyan 4.4

January 9, 2026

Yan siyasan Arewa da malaman addinin Arewa da sarakunan Arewa su ne suka sayar da Arewa ‎ ‎—Naja’atu Muhammad

December 31, 2025

Sheikh gumi ya soki farmakin saman Amurka a Najeriya

December 26, 2025

’Yan majalisar dokokin Kano 2 sun rasu

December 24, 2025

Jinkirin aiwatar da dokokin haraji zai cutar da ma’aikata da talakawa — shugaban kwamitin fadar shugaban ƙasa 

December 22, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2026 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.