Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta tabbatar da kashe sojojinta goma a iyakarta da Burkina Faso
Afrika

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta tabbatar da kashe sojojinta goma a iyakarta da Burkina Faso

February 6, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Gwamnatin sojin ƙasar Niger ta tabbatar da cewa wani harin kwantar ɓauna da ‘yan ta’adda suka kai ya yi sanadin mutuwar sojojinta guda goma a kusa da iyakar ƙasar da Burkina Faso.

A wata sanarwa da gwamnatin sojin ƙasar ta karanto a ranar Laraba da dare, ta bayyana cewa an tura jami’ai zuwa yammacin ƙasar a ranar Litinin domin kama ɓarayin shanu a ƙauyen Takzat.

“A lokacin wannan aikin ne wani gungun masu laifi ya yi wa jami’an tsaron kwanton-ɓauna wanda hakan ya kai ga rasa sojojinmu goma,” in ji sanarwar.

Duk da cewa maharan sun yi ƙoƙarin guduwa amma sojojin sun kama tare da kashe 15 daga cikinsu.

Jamhuriyar Nijar tare da makwabtanta Burkina Faso da Mali sun kwashe fiye da shekaru 10 suna gwabza fada da kungiyoyin ‘yan ta’adda da suka hada da wasu masu alaka da al-Qa’eda da kuma kungiyar Daesh.

Bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a dukkanin kasashen uku a shekarun baya-bayan nan, mahukuntan kasar sun kori sojojin Faransa tare da karkata zuwa ga rundunonin sojojin haya na kasar Rasha domin neman taimakon tsaro.

Kasashen uku sun sha alwashin karfafa hadin gwiwarsu ta hanyar kafa sabuwar kawancen tsaro, wato kawancen kasashen Sahel ta AES.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano

January 12, 2026

Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Kuɗin 2026 Na Naira Tiriliyan 4.4

January 9, 2026

Yan siyasan Arewa da malaman addinin Arewa da sarakunan Arewa su ne suka sayar da Arewa ‎ ‎—Naja’atu Muhammad

December 31, 2025

Sheikh gumi ya soki farmakin saman Amurka a Najeriya

December 26, 2025

Jinkirin aiwatar da dokokin haraji zai cutar da ma’aikata da talakawa — shugaban kwamitin fadar shugaban ƙasa 

December 22, 2025

An Kama ‘Yan Mata Biyu da Laifin Yunkurin Shigar da Miyagun Kwayoyi Cikin Gidan Yari a Kano

December 22, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2026 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.