Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » An yi jana’izar mutanen da harin jirgi ya kashe bisa kuskure a Zamfara
Afrika

An yi jana’izar mutanen da harin jirgi ya kashe bisa kuskure a Zamfara

January 12, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
38610c2b 2f82 42c0 b2ec 284098185089.jpg

Rahotanni daga ƙaramar hukumar Maradun ta jihar Zamfara sun ce an yi jana’izar ‘yan aikin sa kai da wani jirgin yaƙi da ake zargin na sojojiin Najeriya ya kai musu hari bisa kuskure a ƙauyen Tungar Kara.

Wani mazaunin ƙuyen da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa BBC cewa tuni aka yi jana’aizar ‘yan sa kan su 17 da suka mutu a harin, yayin da wasu ke kwance a asibiti.

A ranar Asabar da maraice ne wani jirgi da ake kyautata zaton na sojin ƙasar ne ya kai hari bisa kuskure kan ‘yan sa kai a ƙauyen na Tungar Kara.

Lamarin ya auku ne, yayin da suke ƙoƙarin daƙile wani hari da ƴan bindiga suka kai garin, suna ƙoƙarin kore wasu dabbobi.

Wani mutum – da ya rasa ɗan’uwansa a harin, ya bayyana wa BBC cewa ƴan sa kai da dama ne lamarin ya rutsa da su yayin da suke yunƙurin tunkarar ƴan bindigan da aka ce suna ɓarna a yankin, inda ya kara da cewa ƴan bingidan sun riga sun bar yankin a lokacin da jirgin ya fara ɓarin wuta..

Ya ce: ”Muna zaune sai muka ga jirgi ya nufi wuraren da aka ce ƴan bindigan suke, amma ko a lokacin sun riga wuce. Waɗannan yaran da mutanen da ke ƙasa ne wannan jirgin yake ta harbi, yanzu haka ga ɗan yaya na an kawo mun shi a mace.”

Jami’in watsa labarai na rundunar operation Fansar Yamma da ke gudanar da ayyukan tsaro a yankin arewa maso yammacin Najeriya, Laftanar Kanar Abubakar Abdullahi, inda ya ce zai bincika ya tuntuɓe mu. Haka shi ma mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya shaida mana.

To sai dai wata majiyar gwamnatin jihar, wanda ta buƙaci a sakaya sunanta, ya tabbatar wa BBC aukuwar wannan lamari, amma bai yi wani cikakken bayani ba.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana aniyarta na fara amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira ta AI wajen gudanar da ayyukan zaɓe a ƙasar

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ta kashe fiye da Naira Biliyan Biyu wajen karbo shidar kammala yan asalin Jihar karatun Dalibai Tamanin da Hudu

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ba zata lamunci Jan kafa ba wajen ajiye mutanen da ake tuhuma da laifi a gidan gyaran Hali

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.