Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Zan ƙara buɗe wa ‘yan Nijeriya da kamfanoni hanyoyin samun bashi ga yan kasa – Tinubu
Afrika

Zan ƙara buɗe wa ‘yan Nijeriya da kamfanoni hanyoyin samun bashi ga yan kasa – Tinubu

January 1, 2025
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya ce gwamnatinsa za ta ƙara buɗe hanyoyin samun bashi ga ‘yan ƙasar tare da masana’antu domin ƙarfafa tattalin arziƙin ƙasar a cikin sabuwar shekarar 2025.

A jawabinsa ga ‘yan ƙasar wanda ya wallafa a shafinsa na X, Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta yi wannan ne ta hanyar kafa wani kamfani da zai kasance asusun tabbatar da biyan bashi na ƙasa wato National Credit Gurantee Company domin rage hatsarin ba da bashi ga bankuna da kamfanoni.

“Kamfanin da ake sa ran zai fara aiki kafin tsakiyar shekara zai kasance na haɗin-gwiwa ne tsakanin ma’aikatun gwamnati kamar bankin masana’antu da hukumar ba da bashi ga mutane (Nigerian Consumer Credit Corporation) da kamfanin zuba jari na Nijeriya da ma’aikatar kuɗi ta Nijeriya da ‘yan kasuwa da kuma hukumomin ƙasa da-ƙasa,” in ji shugaban.

“Wannan matakin zai ƙarfafa aminci a tsarin kuɗin ƙasar tare da ƙara hanyar samun bashi da kuma tallafa wa waɗanda ba su cika samun dama ba irin su mata da matasa. Zai kawo ci-gaba da farfaɗo da masana’antu da kuma inganta rayuwar al’umarmu,” a cewar Tinubu.

Haka kuma shugaban ya ce gwamnati za ta yi ƙoƙarin tabbatar da cewa hauhawar farashi ta ragu daga kashi 34.6 cikin 100 zuwa kashi 15 a cikin 100 a shekarar 2025 ta hanyar haɓaka harkar noma tare da inganta haɗa muhimman magunguna a cikin gida.

Shugaban, da ya nemi ‘yan ƙasar su goya masa baya wajen tabbatar da cewa tattalin arziƙin ƙasar ya kai na dala tiriliyon ɗaya, ya ce dole ‘yan ƙasar su inganta biyayyarsu ga ƙasar domin ta iya cim ma muradunta.

“Gaskiyar ‘yan ƙasa da kuma amincewarsu da ƙasar na da muhimmanci wajen nasarar Muradun Sabon Fata,” in ji shugaban wanda ya ce gwamnati za ta mayar da hankali wajen wayar da kan jama’a game da halayen da suka kamata ‘yan ƙasar su kasance suna da su.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.