Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Zazzabin cizon sauro ya kashe mutane dubu 597 a shekarar 2023 – WHO
Afrika

Zazzabin cizon sauro ya kashe mutane dubu 597 a shekarar 2023 – WHO

December 17, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn

Majalisar dinkin duniya ta bayyana cewar har yanzu cutar malaria ko kuma zazzabin cizon sauro na ci gaba da illa a wasu kasashen duniya sakamakon alkaluman da ta gabatar wanda ya nuna cewar akalla mutane miliyan 263 suka harbu da ita a shekarar 2023, yayin da dubu 597 suka sheka lahira.

Sanarwar da kungiyar kawancen Gavi dake yaki da cututtuka ya gabatar, ya ce alkaluman Majalisar dinkin duniya ya nuna cewar an samu karuwar akalla mutane miliyan 11 da suka harbu da cutar daga cikin adadin da aka samu a shekarar 2022, yayin da adadin wadanda suka mutu kuma ke kankankan a tsakanin shekarun biyu.

Wani abin tada hankali shi ne yadda akasarin wadanda suka mutu, wadanda yawansu ya kai kashi 95 na alkaluman da aka gabatar, ya nuna cewar daga Afirka suka fito, abinda ya sa shugaban hukumar lafiya ta duniya, Tedros Ghebreyesus ya yi kirar daukar matakan gaggawa domin tinkarar matsalar.

Ghebreyesus yace babu dalilin da zai sa wani mutum ya mutu sakamakon wannan cutar wadda ke ci gaba da illa da kuma kassara jama’a a yankin Afirka, musamman mata masu juna biyu da kuma kananan yara.

Shugaban hukumar lafiyar ya ce ya zuwa watan Nuwambar da ta gabata, an tabbatar da cewar kasashen duniya 44 sun yi nasarar kawar da cutar malariar baki daya daga cikin su, ya yin da wasu kuma ke ci gaba da daukar matakan cimma irin wannan nasarar.

Jami’in yace daga cikin kasashen duniya 83 da cutar tafi kamari a cikin su, 25 sun bayyana samun raguwar masu kamuwa da cutar, sabanin guda 4 kacal da aka gani a shekara ta 2000.

Ofishin hukumar lafiya ta duniya dake kula da Afirka ya ce alkaluma sun nuna raguwar kashi 16 na yawan mutanen da cutar ke hallakawa tun daga shekarar 2015.

Hukumar lafiyar ta ce kasashe 11 da suka fi samun masu fama da cutar sun gudanar da taro a wannan shekarar inda suka rattaba hannu a kan wata yarjejeniyar taka rawa wajen magance illar da cutar keyi, kuma sun hada da Burkina Faso da Kamaru da Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo da kuma Ghana.

Sauran sun hada da Ghana da Mali da Mozambique da Nijar da Najeriya da Sudan da Tanzania da kuma Uganda.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Hatsaniyar data Faru a Karamar Hukumar Rano wadda ta kai ga Rasuwar DPO da wani mutum daya– ‘Yan sanda Sun Nemi Hadin kai don Dawo da Tsaro a Yankin

May 27, 2025

Babbar kotun shariar musulunci ta yankewa matashin nan Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kashe wasu mutane

May 27, 2025

Hukumar tace fina-finai ta yi nasarar kama wasu na’urori da ake amfani dasu wajan buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin Gargajiya a Jahar Kano

May 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.