Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Za mu tafi hutu daga ranar Talata 18 ga watan Disamban 2024 zuwa 6 ga watan Janairun 2025 – TINUBU
Afrika

Za mu tafi hutu daga ranar Talata 18 ga watan Disamban 2024 zuwa 6 ga watan Janairun 2025 – TINUBU

December 16, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
President Bola Ahmed Tinubu
President Bola Ahmed Tinubu

Majalisar zartarwar Najeriya ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙasar, Bola Tinubu ta sanar da cewa za ta tafi hutu daga ranar 18 ga watan Disamban 2024 zuwa 6 ga watan Janairun 2025.

Majalisar ta bayyana hakan ne bayan wata tattaunawa da ta gudanar yau Litinin a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

A bayanin bayan taron majalisar, hakan na nufin ba za a gudanar da wani taron majalisar ba a tsawon lokacin da za ta kwashe tana hutu.

Majalisar zartaswar Najeriya ta ƙunshi shugaban ƙasa da mataimakinsa da kuma ministoci.

Sanarwar da majalisar ta fitar ta nuna cewa a taron na yau Litinin ta kuma tattauna batun kasafin kuɗin shekarar 2025, da shugaban ƙasar zai gabatar a zauren Majalisar dokokin ƙasar.

Sufuri kyauta:

Majalisar zartaswar ta kuma ayyana sufuri kyauta ga ƴan ƙasar daga ranar 20 ga watan Disamba, 2024 zuwa 5 ga watan Janairun 2025 zuwa sassa daban-daban na ƙasar, kamar yadda gwamnati ta saba yi a lokacin “bukukuwan Sallah da na Kirisimeti.”

Sauya sunan jami’ar Abuja:

“Majalisar ta kuma amince da sauya sunan Jami’ar Abuja zuwa sunan tsohon shugaban ƙasar mulkin soji, Janar Yakubu Gowon, matakin da majalisar ta ce za ta gabatar gaban majalisar dokokin ƙasar domin neman amincewa.”

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yadda dawowar sanyi ya sauya al’amura a Kano

January 12, 2026

Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Kuɗin 2026 Na Naira Tiriliyan 4.4

January 9, 2026

Yan siyasan Arewa da malaman addinin Arewa da sarakunan Arewa su ne suka sayar da Arewa ‎ ‎—Naja’atu Muhammad

December 31, 2025

Sheikh gumi ya soki farmakin saman Amurka a Najeriya

December 26, 2025

Jinkirin aiwatar da dokokin haraji zai cutar da ma’aikata da talakawa — shugaban kwamitin fadar shugaban ƙasa 

December 22, 2025

An Kama ‘Yan Mata Biyu da Laifin Yunkurin Shigar da Miyagun Kwayoyi Cikin Gidan Yari a Kano

December 22, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2026 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.