A wata ganawa da shugabannin hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya jaddada aniyarsa na gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025 cikin tsari da nasara.
Ahugaban ya bayar da tabbacin ne a jawabinsa yayin wani taro da aka gudanar a hedikwatar hukumar NAHCON da ke Abuja.
Farfesa Pakistan ya nuna godiya ga Allah da ya ba da damar gudanar da taron tare da jaddada sadaukarwar hukumar wajan shawo kan kalubale da kuma sake mayar da hankali domin samun damar inganta aikin hukumar.
A cikin jawabinsa, shugaban ya bayyana kalubale da dama da ya tarar lokacin da aka naɗa shi mukamin da suka haɗa da iƙrarin da ba a warware ba da kuma cikas wajen gudanar da ayyukan da suka kawo tasgaro ga ci gaban wasu muhimman ayyuka.
Ya kuma baiwa masu ruwa da tsaki tabbacin ci gaba da kokarin shawo kan matsalolin.
“Alhamdulillah, a yau dukkanmu muna nan a matsayin abokan aiki, muna haɗa kawunanmu wuri guda domin magance ƙalubalen da ke gabanmu da kuma yin aiki a matsayin wata babbar ƙungiya domin tallafawa ɗaya daga cikin shika-shikan Musulunci,” inji Farfesa Pakistan.
Har ilayau ya bayyana wasu daga cikin batutuwan da ake ta cece-kuce da su kawo yanzu, wanda suka haɗa da mayar da Riyal 150 na Saudiyya da rashin da wutar lantarki ingantacciya a lokacin aikin Hajjin 2023.
Farfesa Abdullahi Pakistan ya tabbatar da cewa shugabancinsa na aiki tuƙuru domin ganin an daidaita kuɗaɗen hidimar kashi 2% da aka warewa hukumar alhazai ta jiha dangane da aikin Hajjin 2024.
Shugaban ya kuma yi alƙawarin biyan duk kanin wasu haƙƙoƙi da aka nema waɗanda suka yi daidai da doka, tare da aza harsashin wani sabon babi na ayyukan NAHCON.
Farfesa Saleh ya yi kira ga shugabannnin hukumomin alhazai na jahohi dasu gaggauta sanya kuɗaɗe ga hukumar domin samun damar yin shiri da wuri da suka haɗa da samar da gidaje masu arha da dacewa a Madina, Makkah, Mina da Mashaer.
Ya kuma sanarwa da taron cewa zai fara ziyarce-ziyarce a shiyyoyin kasar nan guda shida domin tattaunawa da malaman addini da sarakunan gargajiya domin samun goyon baya da albarkar aikin Hajjin 2025 da kuma ziyarar farko kafin aikin Hajji a kasar Saudiyya wanda zai gudana a watan Janairun 2025 wanda ya ƙunshi wakilai daga NAHCON da shugabannin hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi wadanda za su halarci tarukan shirye-shiryen aikin Hajji, tare da kammala yarjejeniya da hidimar alhazai, da kuma duba shirye-shirye a Jeddah.
Shugaban hukumar ta NAHCON ya kuma jaddada muhimmancin haɗa kai, inda ya bayyana ma’aikatan NAHCON da shuwagabannin masu ruwa da tsaki na jahohi a matsayin manyan ginshiƙan hukumar.
Ya bukaci masu ruwa da tsaki da su hada kai a matsayin abokan aiki domin cimma manufa ɗaya ta samar da aikin Hajji mai cike da inganci ga alhazan Najeriya.
A cikin kalamansa, “Na zo nan ne da kyakkyawar niyya da kuma tsare-tsare masu yawa na kawo sauyi a fasalin Hukumar.
A jawabin Kwamishinan aiyuka na hukumar, Prince Anofi Olarewaju Elegushi ya bayar da bayanai kan kalandar Hajji ta 2025, inda ya bayyana cewa an raba takardar jagora mai shafuka 51 daga ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya don daidaita ayyukan.
Taron ya kuma tabo batutuwan da ba a warware su ba daga aikin Hajjin 2024 inda Kwamishinan hukumar mai Kula da Ma’aikata da Kudi (PPMF), Aliu Abdulrazak ya bayyana cewa Shugaban hukumar NAHCON ya ba da izinin fara biyan kuɗaɗen da Jihohi ke biya bayan an kammala sulhu da su da sashen kuɗi da Asusu.

