Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » An samu raguwar kamuwa da cutar Malaria a duniya
Afrika

An samu raguwar kamuwa da cutar Malaria a duniya

December 11, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
6753831e 40b9 44c6 af89 5ebaa5e9fe48.png
6753831e 40b9 44c6 af89 5ebaa5e9fe48.png

Wani sabon rahoto da Hukumar Lafiya ta Duniya ta fitar ya nuna cewa an samu raguwar masu kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro wato maleriya a duniya, da kimanin mutum biliyan biyu inda aka samu raguwar masu mutuwa daga cutar tun daga shekarar 2000 kawo yanzu.

Sai dai rahoton ya ce har yanzu akwai miliyoyin mutane da ke fama da wannan cuta a duniya musamman a nahiyar Afirka, inda adadin masu kamuwa da cutar ya kai kashi 95 cikin dari, sakamakon rashin ingantaccen tsarin kiwon lafiya da kuma hanyoyin samar da kariya daga cutar.

Duk da wannan nasarar da aka samu a cikin wadannan Shekarau, Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayana cewa har yanzu cutar zazzabin cizon sauron na ci gaba da shafar mutane da dama a Afirka, musamman mata masu juna biyu da yara kanana wadanda su ne sahun gaba daga cikin masu fuskantar barazana daga wannan cuta.

Daga watan Nuwambar shekarar 2024, an samu kimanin kasashe arba’in da hudu da kuma wani yanki guda daya da suka zama na farko a duniya da hukumar lafiya ta duniya ta ce ta kawar da cutar maleriya dungurungum a cikinsu.

Kazalika, akwai kasashe da dama da ke daf da cimma wannan matsayi. Inda kimanin kasashen ashirn da biyar a yanzu daga cikin kasashe tamanin da uku da al’ummarsu suka fi fama da zazzabin cizon sauro, suka bayyana raguwar matsalar.

Daraktan hukumar Lafiyar, Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce duk da an samu gagarumin ci gaba a wannan bangare na yaki da cutar maleriya a wasu sassan duniya, amma a kasashen Afirka har yanzu akwai fatan da ake da shi na neman mafita daga wannan barazana.

Tun a shekarar 2015 WHO, ta ce an samu cimma kashi 16 cikin 100 na muradun da ake da sun a samun raguwar mace-mace a dalilin cutar ta Maleriya.

Sai dai wata kididdiga da hukumar ta fitar a 2023 ta nuna cewa a duk cikin mutum dubu daya ana samun kashi hamsin da biyu da ke mutuwa sakamakon cutar, abin da ke nuna karuwar masu rasa rayukansu fiye da sau biyu, wanda kuma ya yi hannun riga da muradin nan na shirin kawar da cutar maleriya nan da shekarar 2030.

A farkon wannan shekarar ministocin lafiya da ga kasashen Afirka sha daya da suka hada da Burkina Faso da Kamaru da Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo da Ghana da Mali da Mozambique da Nijar da Najeriya da kuma Sudan, sun yi wani taro inda suka saka hannu kan wata yarjejeniyar da ke fafutukar yaki da maleriya da kuma manufar inganta tsarin kiwon lafiyar kasashen.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana aniyarta na fara amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira ta AI wajen gudanar da ayyukan zaɓe a ƙasar

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ta kashe fiye da Naira Biliyan Biyu wajen karbo shidar kammala yan asalin Jihar karatun Dalibai Tamanin da Hudu

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ba zata lamunci Jan kafa ba wajen ajiye mutanen da ake tuhuma da laifi a gidan gyaran Hali

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.