Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Nijeriya za ta dogara da sayen jiragen yaƙi daga Turkiyya domin kawo ƙarshen ta’addanci – Muhammad Badaru
Afrika

Nijeriya za ta dogara da sayen jiragen yaƙi daga Turkiyya domin kawo ƙarshen ta’addanci – Muhammad Badaru

November 21, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
bad
bad

Ministan Tsaron Nijeriya Mohammed Badaru Abubakar ya ce karshen ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane a Najeriya ya kusa, adaidai lokacin da kasar ke samun karin kayan aikin soja daga Turkiyya.

Minista Badaru ya yi wannan jawabin ne a sansanin sojin saman Nijeriya da ke jihar Katsina a arewacin kasar, yayin kaddamar da jiragen yaki masu saukar ungulu na T129 ATAK guda biyu, wadanda kasar ta saya daga kasar Turkiyya.

“Karshen ayyukan ‘yan ta’adda da ‘yan daba masu dauke da makamai a kasar ya kusa,” in ji Ministan Tsaron Nijeriya a wajen taron a farkon makon nan.

Ya kuma yi kira ga rundunar sojin sama da ta hada kai da sojojin kasa da sauran masu ruwa da tsaki domin samun nasara a kan makiya kasar.

Mista Abubakar ya bukaci jami’an tsaro da su ƙara zage damtse wajen ganin sun kawar da ‘yan ta’adda masu dauke da makamai, da kuma kungiyoyin ta’addanci na Boko Haram da ISWAP, yana mai jaddada cewa suna barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali da walwala.

Nijeriya ta ƙulla yarjejeniya da kamfanin ƙera jiragen yaƙi na Turkiyya, TAI, na sayen jirage masu saukar ungulu na T-129 ATAK guda shida domin bunkasa karfin sojojinta na sama.

Kasar ta Afirka ta Yamma ta samu biyu daga cikin jirage masu saukar ungulu na yaki a watan Fabrairu, biyu kuma a watan Satumba, yayin da ake kan aikin ƙera sauran biyun.

A cikin ‘yan shekarun nan, kasashen biyu sun samu ci gaba sosai, kuma ana sa ran za su rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniyar tsaro ta sama da dala biliyan biyu nan gaba, a cewar majiyoyin.

Jami’an Nijeriya karkashin jagorancin Ministan Tsaro sun ziyarci Turkiyya a watan Fabrairun wannan shekara inda suka tattauna da sakataren masana’antun tsaro na fadar shugaban kasar ta Jamhuriyar Turkiyya Farfesa Dr Haluk Görgün.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana aniyarta na fara amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira ta AI wajen gudanar da ayyukan zaɓe a ƙasar

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ta kashe fiye da Naira Biliyan Biyu wajen karbo shidar kammala yan asalin Jihar karatun Dalibai Tamanin da Hudu

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ba zata lamunci Jan kafa ba wajen ajiye mutanen da ake tuhuma da laifi a gidan gyaran Hali

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.