Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Gwamnatin Kano Zata Fara yiwa Baki mazauna jihar Rijista
Afrika

Gwamnatin Kano Zata Fara yiwa Baki mazauna jihar Rijista

November 5, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
WhatsApp Image 2024 08 23 at 20.00.22
WhatsApp Image 2024 08 23 at 20.00.22

Gwamnatin jihar Kano dake arewacin Najeriya ta kafa kwamitin ƙwararru da zai yi aikin yiwa baƙi ƴan ƙasashen waje mazauna birnin rijista, musamman waɗanda suke gudanar da kasuwanci.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne domin samun alƙaluman mutanen da suka fito daga ƙasashen ƙetare kuma suke gudanar da harkokin kasuwanci a jihar ta yadda za’a haɓɓaka kudin shiga da kuma tsaro da samar da ayyukan yi.

Kwamitin da ke ƙarƙashin ofishin sakataren gwamnatin Kano Dr. Abdullahi Baffa Bichi, zai tattara bayanan baƙin da ke aiki walau na kamfani ko a wata ma’aikata ko kuma kasuwanci.

Shugaban kwamitin, Lawan Isa Kibiya ya ce aikin da za su yi zai taimaka wajen tabbatar da ganin baƙin waɗanda mafi yawa ƴan kasuwa ne su na biyan haraji kamar yadda doka ta yi tanadi.

Ya ƙara da cewa hakan zai bai wa gwamnati ƙwarin gwiwar ‘‘ƙoƙarin ganin ta samar da yadda za ta ba su kariya ta fuskar tsaro’’

Kwamishinan ma’aikatar ciniki ta jihar Kano, Alhaji Adamu Aliyu Kibiya wanda wakili ne a kwamtin ya ce ‘‘aikin bai taƙaita ga buƙatar tattara haraji kaɗai ba, duk duniya akwai ƙa’idoji da aka kafa a doka, waɗanda idan baƙo ya je zai yi kasuwanci ga ƙa’idojin da ya kamata ya bi, sannan su ma ƴan gari ga ƙa’idojin da ya kamata su bi.’’

Ya ƙara da cewa ‘‘idan ka shiga wannan manyan kasuwannin namu, musamman kantin kwari, za ka ga baƙin su ne mafi yawa ke ƙerawa, su yi packaging su kuma yi kasuwanci kai tsaye.’’

Adamu Kibiya, ya kara da cewa ire-iren waɗannan abubuwan gwamnati ta kalla shi yasa ake ƙoƙarin fito da tsarin da zai taimaki al’umma musamman wajen samar da ayyuka da kare martabar kasuwanci: ‘‘Idan muka zura ido mu ka yi gaba to zai zamo nan gaba mun koma maula, mutanen mu sun koma bara, don haka gwmanati ta duba, ta ga dole wadannan abubuwa an taka musu birki.’’

Ya ƙara da cewa tsarin zai tsaftace harkokin kasuwanci a jihar, musamman yadda aka saba samun masu yi wa ƴan kasuwa zambo domin kwashe musu kuɗi, kuma ana samun irin waɗannan bata gari masu aikatawa daga kowanne ɓangare.

Toh sai dai kwamitin ya tabbatar da cewa rijistar ba ta shafi ƴan wasu jihohin da suke zaune a jihar Kano ba, inda ake fatan nan da makonni biyar kwamitin zai mikawa gwamnati rahotansa.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita dake Karamar Hukumar Dutsenma a Jihar Katsina ta tuna da Marigayi Isa Kaita

July 2, 2025

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban Najeriya – Barau I Jibrin

June 26, 2025

Babbar Kotun Tarayya ta yi umarni ga Hukumar EFCC data cigaba da bincike kan filin Musabaka da ake zargin wasu a Jihar Kano sun siyar ba bisa ka’ida ba

May 23, 2025

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta bayyana aniyarta na fara amfani da fasahar ƙirƙirarriyar basira ta AI wajen gudanar da ayyukan zaɓe a ƙasar

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ta kashe fiye da Naira Biliyan Biyu wajen karbo shidar kammala yan asalin Jihar karatun Dalibai Tamanin da Hudu

May 23, 2025

Gwamnatin jihar Kano ba zata lamunci Jan kafa ba wajen ajiye mutanen da ake tuhuma da laifi a gidan gyaran Hali

May 19, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Kano

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

By WafsymApril 13, 2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta bayana Dalilan yin Gwanjon…

Hukumar tace fina-finai ta haramtawa Usman Sojaboy da wasu mata biyu shiga harkokin Film ko waka a Kano

January 20, 2025

Madrid ko Barca: Wa zai lashe Spanish Super Cup?

January 12, 2025

Barca ta kara rashin nasarar ɗaukaka kara kan yi wa Olmo rijista

December 31, 2024
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.