Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano
Afrika

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
AB
AB

Gwamnatin jihar Kano dake arewacin Najeriya ta yi watsi da rahotannin da ake yaɗawa cewa akwai rashin jituwa tsakanin Gwamnan Jihar Abba Kabir Yusuf da kuma jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

A ranar Litinin ne jaridar Daily Nigerian ta fitar da wani labari wanda ke zargin cewa gwamnan Kano Abba Kabir ya daina ɗaukar kiran wayar uban gidansa Sanata Rabiu Kwankwaso, lamarin da hakan ya tayar da ƙura a kafofin sada zumunta.

Sai dai a wata sanarwa da babban mai taimakawa gwamnan Kano kan kafofin sada zumunta Salisu Yahaya Hotoro ya fitar, ya ce babu wata rashin jituwa tsakanin Gwamna Abba da mai gidan nasa Kwankwaso.

“Gwamna Abba K Yusuf ya himmatu sosai wajen tabbatar da akidu da hangen nesa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP). Ya himmatu wajen samar da hadin kai a cikin jam’iyyar tare da yin aiki tare da dukkan ‘ya’yan jam’iyyar ciki har da Kwankwaso domin cim ma burinmu,” kamar yadda sanarwar ta ƙara da cewa.

“Wannan zargin ba gaskiya bane kuma karkatar da hankali ne sakamakon Abba yana da ladabi da alaƙa mai kyau da Rabiu Kwankwaso, inda yake kallonsa a matsayin jagora a jam’iyya da kuma tafiyarsa ta siyasa. Duk wata magana ta ɓaraka a tsakaninsu batu ne kawai na zuzutawa, amma ya saɓa wa mu’amularsu ta aiki,” in ji sanarwar.

A ‘yan kwanakin nan ana ta samun raɗe-raɗin rashin jituwa a tsakanin gwamnan na Kano da kuma Kwankwaso inda har wasu da ba a tabbatar da ko su wane ne ba suka fitar da wata tafiya mai suna Abba Tsaya da Kafarka, wadda ke nufin Abban ya ƙaurace wa Kwankwaso.

A ranar Litinin ne Dan majalisar wakilan jihar daga karamar hukumar Dala Aliyu Sani Madakin Gini da takwaransa na kananan hukumomin Rano da Bunkure da kuma Kibiya a majalisar wakilan kasar suka sanar da barranta kansu da tafiyar Kwankwasiyya a jihar.

Featured
Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Yawan Al’umma Na Iya Tsananta Matsalar Tsaro a Nijeriya-Bankin Duniya

October 20, 2025

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

October 20, 2025

Kano: KIRS Ta Fitar Da Sabon Tsarin Biyan Haraji Ta Hanyar Fasahar Zamani

October 6, 2025

Takardar Sakandire Ta Isa Bayar Da Damar Rike Mukamin Siyasa — Shehu Sani

October 6, 2025

Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024

October 6, 2025

NDLEA ta kama tarin ƙwayoyi da ake shirin safararsu zuwa Birtaniya

October 6, 2025
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Tsohon Gwamna Na Fuskantar Bincike Kan Zargin Hannu a Shirin Juyin Mulki

By WafsymOctober 20, 2025

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamna daga wani yanki na kudu na ƙasar nan wanda…

Hawan Jini: Ƙungiyoyi Sun Yi Gargadi Kan Yaduwar Cutar a Nijeriya

September 27, 2025

Barkewar Cututtuka Uku Sun Tayar da Hankalin Hukumomin Lafiya a Nijeriya ‎

September 27, 2025

DALILAN DA YASA MUKAYI GWANJON TSAFFIN MOTOCIN DA MUKE GUDANAR DA AIKIN MU- NDLEA

April 13, 2025
© 2025 WDN HAUSA
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.