Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Sabon shugaban Iran yana neman hanyar sasantawa da ƙasashen duniya biyo bayan mayar da ƙasar saniyar ware.
Asia

Sabon shugaban Iran yana neman hanyar sasantawa da ƙasashen duniya biyo bayan mayar da ƙasar saniyar ware.

August 23, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
iran2
iran2

A ranar 11 ga watan Agusta ne, sabon zaɓaɓɓen shugaban na Iran Masoud Pezeshkian ya gabatar da sunayen mutanen da yake so a ba ministoci a gaban majalisar dokokin ƙasar domin neman ƙuri’ar amincewa.

Dangane da dokar Iran, kakakin majalisar ƙasar zai karanta takardar gabatarwa ta shugaban ƙasar, inda bayan haka sai sauran takardu su biyo baya waɗanda za a miƙa su ga kwamitocin da suka dace domin dubawa.

Waɗannan kwamitocin an kafa su ne domin tantance cancanta da takardu da asali da kuma shawarar bayar da ma’aikatar da ta dace ga kowane minista tare da gabatar da bincikensu ga kakakin majalisa. Haka kuma za a buga takardun wannan rahoto tare da miƙa su ga duka mambobin majalisa domin bitarsu.

Mako ɗaya bayan gabatarwar ta gwamnati, za a yi zama daban-daban a majalisa domin tafka muhawara dangane da tsare-tsare da shirye-shirye na gwamnati tare da gudanar da ƙuri’ar amincewa dangane da ministocin.

A cikin wannan lokacin, ministocin da aka zaɓe su za su aika da shirye-shiryensu ga kwamitocin da suka dace da kuma mayar da martani dangane da duk wata buƙata daga mambobin kwamitin.

Ana saran matakin zai kai ga samun kuri’un amincewa da kowane minista, sannan kuma za a kada kuri’ar amincewa ga daukacin majalisar ministocin kasar.

Majalisar ministocin da Pezeshkian ke son ya kafa

Gabatar da sunayen ministoci da shugaban ya yi ya jawo zazzafar muhawara a kafofin watsa labarai na Iran, inda akasarinsu suke mayar da hankali dangane ko yanayin waɗanda aka zaɓa a ministoci ya zo daidai da alƙawarin da Pezeshkian ya yi a lokacin yaƙin neman zaɓe dangane da irin mutanen da zai yi aiki da su.

Musamman ma, matsakaitan shekarun mambobin majalisar ministocin ya kai kusan shekara 60. Mace daya ce kawai aka zaba, kuma majalisar ministocin kasar mai rinjayen ‘yan Shi’a ba ta da wakilcin ‘yan Sunna.

Idan aka yi la’akari da manyan kalaman da ya rinƙa yi dangane da batun kawo sauyi, da alama majalisar ministocin da ake son kafawa ta yi kama da mai matsakaicin ra’ayi, ta karkata ga ra’ayin mazan jiya maimakon wacce aka yi alkawarin kawo sauyi.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim

April 29, 2026

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026

An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje

April 24, 2026

El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi

April 21, 2026

Dole Najeriya ta samu tsaro – Babban hafsan tsaro

April 20, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.