Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Ambaliyar ruwa ta katse wasu manyan hanyoyin birnin Yamai a Jamhuriyar Nijar
Afrika

Ambaliyar ruwa ta katse wasu manyan hanyoyin birnin Yamai a Jamhuriyar Nijar

August 23, 2024
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
flood niger
flood niger

Wasu manyan hanyoyin fita da shiga na birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar mai kimanin mutum miliyan 1.5 sun kusan katsewa baƙi ɗaya, kana sama da mazauna birnin mutum 11,500 ne iftila’in ambaliyar ruwan sama ya shafa.

A watanni uku da suka wuce, ambaliyar ta yi sanadiyar mutuwar mutane 217 a faɗin ƙasar kana ta shafi sama da mutane 350,000, a cewar gwamnatin mulkin soji ta Nijar.

Da farko dai birnin Yamai ya tsira daga sauran yankunan kudu maso yammacin Nijar, amma a yanzu, kwale-kwale ne suka maye gurbin ƙanana da manyan motoci da babura wajen jigilar mutane da kayayyaki a kan hanyoyi.

Don samun damar isa zuwa ga sauran sassan ƙasar, ”dole sai mutum ya yi amfani da kwale-kwale tare da fatan samun abin hawa idan ya isa ɗaya bangaren,” in ji Habibulaye Abdoulaye, wani mazaunin wata unguwa da ke kewaye da ruwa.

Yawancin kamfanonin sufuri a Yamai sun dakatar da zirga-zirga zuwa sauran sassan Nijar.

Yayin da yake kallon yadda ambaliyar ruwan ke gudu ta gefen birnin, wani direban mota Ali Adamou ya shaida wa kamfanin dillacin labarai Faransa AFP cewa ruwan ya tafi da motarsa tare da wasu guda hudu.

“Na kusan mutuwa a lokacin da wata ƙaramar motar bas ta nutse,” in ji A damou

Gyaran hanyoyi

Masu tuƙa ƙananan jiragen ruwa suna karɓar CFA 500 kan duk jigilar da suka yi sai kuma ‘yan sanda da kwale-kwalen sojoji waɗanda suke taimakawa wajen jigilar mazauna da suka maƙale.

Daga gabashin babban birnin ƙasar, kamfanin gine-gine na ƙasar Faransa Sogea-Satom na ƙoƙarin sake buɗe hanyar ƙasa ta ɗaya, babbar hanyar da ta kai tsawon kilomita 1,500.

A gaɓar kogin Neja da ke birnin Yamai, masu aikin tono suna can suna aikin samar da hanyoyin wucewar ruwan, yayin da masu aikin sa kai da sojoji suke zagayawa don toshe wurare da ruwan ya yi wa illa da yashi.

A kwanakin baya ne aka sake buɗe hanya ɗaya tilo ta Tera da manyan motoci suke wucewa daga Yamai zuwa arewacin Burkina Faso.

“Hukumomin jihar suna yin dukkan mai yiwuwa don maido da zirga-zirgar ababen hawa,” in ji Ministan Sufuri, Kanar Salissou Mahaman Salissou.

Sai dai hukumomin Nijar na fargabar tsawaita zirga-zirgar na iya haifar da ƙaranci man fetur.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Gwamnan Kano ya sauke shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Abdullahi Musa daga mukaminsa

March 11, 2026

Sojojin UAE biyu sun mutu a hatsarin jirgin sama – Ma’aikatar tsaro

March 10, 2026

Mojtaba Khamenei Ya Gaji Mahaifinsa A Matsayin Jagoran Addinin Iran

March 9, 2026

Farashin litar man fetur ya zarce naira dubu 1 a sassan Najeriya

March 9, 2026

Mutanen da ake hasashen za su maye gurbin Mataimakin Gwamnan Kano

March 7, 2026

Yakin Amurka/Isra’ila da Iran: Lallai da ni za a zaɓi sabon shugaba a Iran – Trump

March 6, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Bincike Na Musamman

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

By WafsymMarch 11, 2026

Sabbin matakan da Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dauka na fara shirin tsige Mataimakin Gwamna,…

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026

Kasuwannin Dabbobi A Kano Na Ƙara Bunƙasa, Amma Amfani da “Sha Ka Fashe” Na Barazana Ga Lafiyar Jama’a ‎ ‎—Rahoto na musamman  ‎

February 27, 2026

KANO: Farashin Kayan Masarufi Ya Yi Tashin Gwauron Zabi Gabanin Shigowar Azumin Ramadan ‎ ‎

February 12, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.