Ƙasar Koriya ta Kudu ta bayyana cewa za ta mayar da martani kan harin da aka kai wa wani jirgin dakon kaya mallakin kamfanin ƙasarta a Tekun Fasha, bayan bincikenta ya gano waɗanda ke da hannu a harin.
A cikin wata sanarwa da Koriya ta Kudu ta fitar, gwamnatin ƙasar ta yi Allah-wadai da harin tare da cewa tana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.
Dalilin da ya sa na maida akwatin zaɓena Abuja – Pantami
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa ƙwararrun Koriya ta Kudu sun gudanar da binciken farko domin tantance irin ɓarnar da aka yi wa jirgin. Ma’aikatar harkokin wajen Koriya ta Kudu ta kuma wallafa hotunan jirgin da ya lalace sakamakon harin da aka kai masa a yankin Tekun Fasha.
Jirgin dakon kayan mai suna HHM Namo, wanda kamfanin sufurin ruwa na HMM ya mallaka, ya fuskanci hari ne da wasu makamai guda biyu da ba a san ko su waye suka harba ba a ranar 4 ga watan Mayu yayin da yake wucewa ta mashigar Hormuz.
Rahotanni sun ce babu wanda ya rasa ransa a harin.
Tun da farko dai Iran ta musanta hannu a harin da gobarar da ta tashi a cikin jirgin.

