Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim
Afrika

HARIN FARM CENTRE: Kada A Bari Rikicin Siyasa Ya Lalata Tattalin Arzikin Kano — Abbas Ibrahim

April 29, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260429 WA0002

Harin da wasu da ake zargin ’yan daba masu alaƙa da siyasa suka kai Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Cente da ke Kano ya janyo hankalin jama’a, inda ake ganin lamarin wata babbar barazana ce ga zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a jihar, musamman yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.

‎Lamarin ya faru ne a ranar Litinin, 27 ga Afrilu, 2026, inda aka ga yadda wasu suka mamaye kasuwar, suka yi sace-sace, tare da lalata dukiyoyi ciki har da motoci da babura. Haka kuma, mutane da dama sun samu raunuka a yayin harin

‎Kasuwar Farm Centre na daga cikin manyan cibiyoyin kasuwancin wayoyi da fasahar sadarwa a Arewacin Najeriya, wadda ke jan hankalin ’yan kasuwa daga sassa daban-daban na ƙasar har ma da maƙwabta.

‎Saboda haka, duk wata barazana ga kasuwar na da tasiri kai tsaye ga tattalin arzikin Kano.

‎Wannan lamari ya sake jefa ’yan kasuwa cikin damuwa, musamman duba da cewa da yawa daga cikinsu har yanzu ba su gama murmurewa daga gobarar da ta taba aukuwa a kasuwar ba.

‎Har ila yau, kasancewar ofishin fasfo na Kano yana kusa da wurin da lamarin ya faru, ya ƙara nuna yadda batun tsaro ke bukatar kulawa ta musamman, domin irin wannan tashin hankali na iya jawo damuwa ga baƙi da masu zuba jari.

‎Ko da yake wani ɗan siyasa da ake danganta shi da harin ya musanta hannu a ciki, masu sharhi na ganin cewa lamarin ya nuna yadda rikicin siyasa ke ƙara tsananta, musamman idan aka kasa dakile mabiyan ’yan siyasa.

‎’Yan sanda sun yi gaggawar ɗaukar mataki, inda suka yi amfani da hayaki mai sa hawaye domin tarwatsa masu tayar da hankalin, tare da kama mutum shida. Sai dai duk da haka, ana ganin har yanzu akwai gibi a ɓangaren tsaro a irin wannan muhimmiyar kasuwa.

‎Masana sun shawarci gwamnatin Kano da ta ƙara ƙarfafa jami’an tsaro, musamman rundunar ’yan sintiri da Hukumar Tsaron Unguwanni, domin tabbatar da tsaro a muhimman wuraren kasuwanci.

‎Shawarwari

‎Masu ruwa da tsaki sun bayar da wasu shawarwari kamar haka:

‎’Yan siyasa su rungumi zaman lafiya tare da jan kunnen mabiyansu

‎A binciki lamarin tare da hukunta duk wanda aka samu da laifi

‎A ƙara tsaro a Farm Centre ta hanyar haɗin gwiwar jami’an tsaro

‎Gwamnati ta samar da rundunar gaggawa don kare kasuwanni

‎A ƙarfafa wayar da kai kan muhimmancin zaman lafiya a siyasa

‎Msu sharhi na ganin Kano na fuskantar wani muhimmin lokaci, inda dole ne a ɗauki matakan kare zaman lafiya da martabar jihar a matsayin cibiyar kasuwanci a Arewa.

‎Sun jaddada cewa, bai kamata a bar rikicin siyasa ya zama sanadin lalacewar dukiyoyi da rayuka ba, tare da kira ga kowa da kowa da ya mara baya wajen tabbatar da zaman lafiya kafin zaɓen 2027.

 

Comrade Abbas Ibrahim writes from Kano and can be reached @ abbasibrahim664@gmail.com

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026

An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje

April 24, 2026

El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi

April 21, 2026

Dole Najeriya ta samu tsaro – Babban hafsan tsaro

April 20, 2026

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.