Close Menu
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
Facebook X (Twitter) Instagram YouTube WhatsApp TikTok Telegram
WDN HAUSAWDN HAUSA
  • Labaran Duniya
    • Afrika
    • Turai
    • Asia
    • Arab
  • Rahotanni
  • Siyasa
  • Shirye-Shirye
    • Bincike Na Musamman
    • Shirye-Shiryen Radio
    • Shirye-Shiryen Siyasa
  • Wasanni
  • Bidiyo
  • Game da Mu
    • Tuntube Mu
    • Privacy Policy
WDN HAUSAWDN HAUSA
Home » Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

April 25, 2026
Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram LinkedIn
IMG 20260423 WA0008

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka a Jihar Kano na da alaƙa da shan miyagun ƙwayoyi da fataucinsu, lamarin da ya nuna yadda matsalar ke da nasaba da rikice-rikicen daba da a yankin.

Rahoton sirri da aka samu ya nuna cewa shan miyagun ƙwayoyi ya zama babban abin da ke ƙarfafa ƙungiyoyin daba, waɗanda ke shiga rikice-rikicen tashin hankali, hare-haren makamai da faɗace-faɗacen titi a sassan jihar.

Rahotan, wanda rundunar ‘yansandan Jihar Kano ta tattara ƙarƙashin jagorancin kwamishinan ‘yansanda Ibrahim Adamu Bakori, ta nuna cewa an kama mutane 3,081 da ake zargi da manyan laifuka a shekarar 2025, inda da dama daga cikinsu ke da alaƙa da harkokin miyagun ƙwayoyi.

Rahoton ya bayyana halin da ake ciki a matsayin abin damuwa, inda cibiyoyin fataucin miyagun ƙwayoyi ke ci gaba da bunƙasa tare da ƙara ruruta laifukan tashin hankali da ke haddasa mace-mace, jikkata mutane da lalata dukiyoyi.

Sai dai rahoton ya yi gargaɗin cewa matsalar na iya ƙara tsananta idan ba a ɗauki mataki mai ƙarfi ba, yana mai cewa rashin ɗaukar mataki zai iya haifar da ƙarin ƙaruwar laifuka da barazana ga tsaron jama’a.

Bincike ya kuma nuna cewa ƙungiyoyin daba da ke da alaƙa da Fadan Daba na samun goyon baya daga hanyoyin rarraba miyagun ƙwayoyi, waɗanda ke samar musu da kuɗi da tallafi.

Domin shawo kan matsalar, ‘yan sanda sun ba da shawarar kafa rundunar haɗin gwiwa da za ta haɗa da ‘yan sanda, hukumar NDLEA, ƙungiyoyin sa-kai da sauran hukumomin tsaro domin gano masu laifi, kama su tare da gurfanar da su a gaban kotu, da kuma lalata hanyoyin fataucin miyagun ƙwayoyi.

Rahoton ya jaddada cewa amfani da ƙarfi kaɗai ba zai wadatar ba, inda ya buƙaci a haɗa da shirye-shiryen wayar da kai da kuma gyaran halayen masu shaye-shaye. Haka kuma an ba da shawarar gudanar da yaƙin neman wayar da kai a faɗin jihar, tare da haɗa kan sarakunan gargajiya, malamai da shugabannin al’umma.

Share. Facebook Twitter LinkedIn Telegram Email WhatsApp

Labarai masu alaka

Sarki Sunusi ya caccaki gwamnatin tarayya kan cigaba da ciyo bashi duk da janye tallafin mai

April 24, 2026

An tabbatar da naɗin Dr Muttaqha Darma a matsayin sabon ministan gidaje

April 24, 2026

El-Rufa’i ya sake zargin yunƙurin kama shi

April 21, 2026

Dole Najeriya ta samu tsaro – Babban hafsan tsaro

April 20, 2026

‘Ba zan ba ‘yan Najeriya kunya ba’ – Shugaba Tinubu

April 17, 2026

Wannan ce takarata ta ƙarshe – Atiku

April 15, 2026
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Babu ɓaraka ko rikici tsakanin Abba da Kwankwaso – Gwamnatin Kano

November 4, 202415

Fagen Wasannin DNN Hausa

October 22, 20248

Dorinar ruwa ta lakume mai gadin gidan gonar Sarkin Yauri na jihar Kebbi.

September 23, 20247

Zamu ba wa fannin lafiya fifiko fiye da komai a karamar hukumar Dala – Alh. Surajo Ibrahim Iman

December 20, 20246
SOCIAL MEDIA
  • Facebook
  • Twitter
  • Instagram
  • YouTube
  • TikTok
  • WhatsApp
  • LinkedIn
  • Telegram
KADA A BAKU LABARI
Afrika

Kashi 70 na laifukan da ake aikatawa a Kano sanadin shaye-shaye ne – Ƴansanda

By WafsymApril 25, 2026

Wani rahoton ‘yansanda ya bayyana cewa sama da kashi 70 cikin 100 na manyan laifuka…

Tsarin Tallafin Magani Na Hukumar KACHMA Na Neman Zama Matsala Ga Marasa Lafiya A Kano

April 2, 2026

Yunkurin Tsige Mataimakin Gwamnan Kano Da Matsayin Doka

March 11, 2026

RAHOTON MUSAMMAN: Tasiri Da Kalubale Rundunar Kano Neighbourhood Watch — Abin da Rahotanni ke Nuna wa Bayan Fara Aiki

March 9, 2026
© 2026 WDN HAUSA. Developed by: ENGRMKS & CO.
  • Facebook
  • Instagram
  • LinkedIn
  • Telegram
  • Twitter
  • Tiktok
  • Youtube

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.